Gwamnan Jihar Oyo kuma mamba a Kungiyar Gwamnonin jam’iyyar PDP, Injiniya Seyi Makinde, ya bayyana cewa fitar tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, daga jam’iyyar ba zai haifar da wata tangarda ba ga ci gaban jam’iyyar PDP.
Makinde ya bayyana haka ne a ranar Laraba, yayin wata tattaunawa da manema labarai a birnin Akure, bayan da ya gabatar da jawabin musamman a wajen taron tunawa da cika shekaru 10 da naɗin sarauta na Mai Martaba Oba Aladetoyinbo Aladelusi, Deji na Akure.
Ya ce: “Ba na ganin hakan zai kawo koma baya ga PDP a matsayin jam’iyya. PDP cibiya ce, kowa na da ‘yancin shiga da fita yadda ya ga dama.”
A gefe guda kuma, Cif Bode George, ɗan kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya danganta fitar Atiku daga jam’iyyar da burinsa na zama shugaban ƙasa a 2027, wanda ya bayyana da cewa burin ya wuce kima.
Ficewar Atiku daga PDP ba zai girgiza mu ba – Gwamna Seyi Makinde
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
