Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan rawar da ake zargin Kwamishinan Sufuri na jihar, Alhaji Ibrahim Namadi, ya taka a sakin wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, Sulaiman Aminu Dan Wawu.
Gwamnan ya dauki wannan mataki ne bayan samun ƙorafe-ƙorafe daga al’umma, biyo bayan bayyana sunan kwamishinan a wasu takardu na kotu da aka yi amfani da su wajen sakin wanda ake zargin.
Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar.
Sanarwar ta ce Gwamna Abba ya kafa kwamitin bincike na musamman ƙarƙashin jagorancin Barista Aminu Hussain, mai ba shi shawara kan harkokin shari’a da kundin tsarin mulki don tabbatar da gaskiya da adalci.
Gwamnan Kano ya ba da umurnin binciken kwamishinansa da ake zargin ya yi belin dilan miyagun kwayoyi
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
