Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedGwamnan Kano ya roki Tinubu da ya bude boda

Gwamnan Kano ya roki Tinubu da ya bude boda

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya roki shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu da ya bude boda domin a samu wadatar abinci a Nijeriya baki daya. 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar ban girma da shugaban hukumar kwastam, Adewale Adeniyi, ya kai masa ranar Litinin a Kano.

Gwamna Abba Kabir-Yusuf, ya koka kan mawuyacin halin da ‘yan Najeriya ke ciki sakamakon matsi da tattalin arzikin kasar ke ciki, ya ce sake bude iyakokin zai taimaka wajen magance hauhawar farashin kayayyaki da kuma saukar da farashin su.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata