Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedGwamnatin tarayya ta fitar da naira biliyan 6.7 don magance matsalar yaran...

Gwamnatin tarayya ta fitar da naira biliyan 6.7 don magance matsalar yaran da basa zuwa makaranta a Nasarawa

 

Bola Ahmad Tinubu

Gwamnatin tarayya ta hannun hukumar kula da ilimin bai daya ta kasa UBEC, ta bayar da kudi naira biliyan 6.7 na kula da makarantar Smart School ga gwamnatin jihar Nasarawa domin magance matsalar yaran da basa zuwa makaranta a fadin kananan hukumomi 13 na jihar.

Daily Trust ta ruwaito cewa sabuwar makarantar da aka  kaddamar a ranar 24 ga Mayu, 2024, an yi ta ne da nufin inganta yanayin ilimin makarantun firamare da kananan sakandare na gwamnati a fadin Nijeriya.

Babbar sakatariyar hukumar UBEC Aisha Garba ce ta bayyana hakan bayan ta duba makarantar UBEC da ke birnin Lafiya da kuma makarantar da aka gyara a karamar hukumar Akwanga a jihar Nasarawa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata