Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in ƙasar.
A cewar Daraktar Yada Labarai ta Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Hajiya Folasade Boriowo, wacce ta fitar da sanarwar a madadin Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, gwamnatin ta sake jaddada kudirinta na farfaɗo da harkar ilimi a manyan makarantu ta hanyar ƙarin tallafin kuɗi, gyaran manufofi, da ci gaba da tattaunawa da ƙungiyar ASUU da sauran ƙungiyoyin jami’o’i.
DCL Hausa ta ruwaito cewa, Dokta Alausa ya bayyana hakan ne yayin da yake bayani kan yadda tattaunawa ke gudana da ƙungiyoyin malaman jami’a da na sauran cibiyoyin ilimi.
Ya ce Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya dage wajen warware matsalolin da suka daɗe suna damun malaman jami’o’i da inganta walwalarsu ta hanyar gaskiya da tsari mai ɗorewa.
Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta riga ta saki ₦2.311bn, wanda ke zama kashi na 8 na biyan bashin albashi da karin girma na malaman, ta hannun Ofishin Akanta-Janar na Ƙasa (OAGF).
Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
