Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi...

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in ƙasar.

A cewar Daraktar Yada Labarai ta Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Hajiya Folasade Boriowo, wacce ta fitar da sanarwar a madadin Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, gwamnatin ta sake jaddada kudirinta na farfaɗo da harkar ilimi a manyan makarantu ta hanyar ƙarin tallafin kuɗi, gyaran manufofi, da ci gaba da tattaunawa da ƙungiyar ASUU da sauran ƙungiyoyin jami’o’i.

DCL Hausa ta ruwaito cewa, Dokta Alausa ya bayyana hakan ne yayin da yake bayani kan yadda tattaunawa ke gudana da ƙungiyoyin malaman jami’a da na sauran cibiyoyin ilimi.

Ya ce Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya dage wajen warware matsalolin da suka daɗe suna damun malaman jami’o’i da inganta walwalarsu ta hanyar gaskiya da tsari mai ɗorewa.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta riga ta saki ₦2.311bn, wanda ke zama kashi na 8 na biyan bashin albashi da karin girma na malaman, ta hannun Ofishin Akanta-Janar na Ƙasa (OAGF).

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata