DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Tuesday, July 7, 2026
HomeLabaraiZa mu hada kai wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya...

Za mu hada kai wajen magance matsalar tsaron da ta addabi Nijeriya – sabbin hafsonshin tsaron Nijeriya

Sabbin hafsoshin tsaron Nijeriya sun ce za su yi aiki tare domin magance dukkan barazanar tsaro a faɗin kasar, tare da kare martabar ƙasar a kowane fanni.

Jaridar Daily Trust, ta rawaito cewa Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin sabbin hafsoshin da shugaban Tinubu ya tura dasu don amincewa a ranar Laraba.

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya Janar Oluyede, ya bayyana cewa akwai buƙatar Nijeriya ta kafa masana’antar samar da makamai a cikin gida domin rage dogaro da na kasashen waje.

A cewarsa siyan kayan yaki daga kasashen waje akwai tsada sossai, don haka ya kamata a fara kerasu a gida Nijeriya.

Kazalika ya nemi a sake fasalin rundunar ‘yan sanda don rage nauyin da ake dora wa sojoji wajen gudanar da ayyukan da bai kamata su yi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata