Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuGwamnoni na shan suka na rashin taɓuka abin a zo a gani...

Gwamnoni na shan suka na rashin taɓuka abin a zo a gani duk da karɓar Tiriliyan 9 daga asusun FAAC a 2025

Duk da samun kimanin Naira tiriliyan 9 daga rabon hukumar rarraba kudaden shiga na tarayya (FAAC) a shekarar 2025, gwamnonin jihohi na fuskantar suka daga ƙungiyoyin ƙwadago, ƙungiyoyin fararen hula da jam’iyyun adawa, bisa zargin cewa akwai tazara mai faɗi tsakanin karuwar kudaden shiga da ƙarancin ayyukan jin daɗin jama’a.

Bincike kan bayanan rarraba kudaden Asusun Tarayya da Hukumar Kididdiga ta Ƙasa (NBS) ta wallafa, wanda jaridar The PUNCH ta tattara, ya nuna cewa rabon FAAC ga jihohi ya ƙaru da sama da N2tn cikin shekara guda.

Wannan ya jawo suka daga ƙungiyoyin ƙwadago da jam’iyyun adawa.

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi gargaɗin cewa, duk da ƙarin kudaden da jihohi ke samu, ba a ga canji mai ma’ana a rayuwar jama’a ba, tana danganta hakan da raunin shugabanci, fifiko marar dacewa, da cin hanci da rashawa a matakin jihohi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata