A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi, ya ce shi yaki da yunwa, fatara, da mummunan yanayin kiwon lafiya da ilimi a Nijeriya shi ya ke sha’awar yi.
Obi ya bayyana haka ne bayanda ya ziyarci Bishop na cocin Anglican Diocese na Kubwa a Abuja a ranar Litinin dinnan inda ya jaddada cewa ba shi da burin samun wani matsayi.
Peter Obi dai shi ne ya zo na uku bayan Shugaba Tinubu da Atiku Abubakar a jam’iyyar PDP a zaben 2023, inda da dama ke ganin cewa hadakar hadin gwiwa tsakaninsa da Atiku da sauran jam’iyyun adawa za ta iya kai bantensu a zaben shugaban kasa na 2027.
