Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuHukumar EFCC ta gayyaci Abubakar Malami

Hukumar EFCC ta gayyaci Abubakar Malami

Tsohon Babban Lauyan Gwamnatin Nijeriya, Abubakar Malami ya bayyana cewa zai halarci gayyatar da Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arziki zagon kasa ta yi masa domin yin bayani kan wasu al’amura da ake bincike a kansu.

Malami, a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce a matsayinsa na ɗan ƙasa mai bin doka da oda, ya dauki matakin amsa wannan kira ba tare da wani jinkiri ko tangarda ba.

Ya ce ya dade yana tsayawa kan gaskiya da riƙon amana a aikinsa na hidimar jama’a, tare da tabbatar wa ’yan Nijeriya cewa zai rika sanar da su duk wani ci gaban da zai biyo bayan wannan lamari.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata