Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiINEC za ta fara rajistar masu kada kuri’a ta intanet daga 18...

INEC za ta fara rajistar masu kada kuri’a ta intanet daga 18 ga Agusta

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeriya INEC ta sanar da cewa za ta fara rajistar masu kada kuri’a ta dindindin ta hanyar yanar gizo daga ranar 18 ga Agusta, 2025, a fadin kasar nan.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar ban girma da shugabannin hukumar wayar da kan jama’a ta kasa NOA suka kai ofishin INEC da ke Abuja.

Farfesa Yakubu ya kara da cewa za a fara rajistar masu kada kuri’a ta kai tsaye mako guda bayan fara na intanet.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

6 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata