Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedIPMAN ta musanta jita-jitar da ake yadawa cewa tana adawa da rage...

IPMAN ta musanta jita-jitar da ake yadawa cewa tana adawa da rage farashin man fetur da Dangote, NNPC suka yi

Kungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya ta musanta ikirarin da aka yi na cewa tana adawa da rage farashin man fetur da matatar Dangote da kamfanin mai na Nijeriya suka yi.

Wani mai taimaka wa tsohon shugaban kasa Reno Omokri, a wani sako da ya wallafa a shafin sa na X,a daren ranar Asabar, ya yi zargin cewa kungiyar IPMAN na adawa da gwamnatin tarayya ne saboda ragin kudin man fetur da Dangote da NNPC.

Ya rubuta cewa, a karon farko a tarihin Nijeriya,kungiyar ‘yan kasuwar man fetur IPMAN, suna nuna adawa da gwamnatin Nijeriya saboda man fetur din NNPC da na matatar Dangote yana da arha har man da suke shigo da su ke janyo musu asarar kudi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata