Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto (UDUS) ta sanar da cewa za ta karrama fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa, wanda za a ba shi digirin girmamawa na Doctor of Letters (D.Litt), Honoris Causa.
Wannan karramawa na zuwa ne bisa jajircewarsa wajen ilimi, gyaran zamantakewa, da kuma kokarinsa na yada zaman lafiya a Najeriya da ma kasashen waje.
Shugaban Jami’ar Farfesa Bashir Garba ne ya bayyana hakan, a yayin taron manema labarai gabanin bikin cikar jami’ar shekaru 50 da kuma yaye daliban da suka kammala karatu karo na 42.
Haka kuma, tsohon Shugaban Sojojin Najeriya, Laftanar Janar Faruku Yahaya (Rtd.), zai samu lambar girmamawa ta Doctor of Science (D.Sc.), Honoris Causa, bisa gudummawarsa ga harkokin tsaro da kare martabar kasa.
Jami’ar ta bayyana cewa wannan karramawa wani yunkuri ne na girmama mutanen da suka sadaukar da rayuwarsu wajen raya kasa, ilimi da zaman lafiya.
Bikin zai kasance babban abin tarihi yayin da dubban dalibai za su karɓi takardunsu, tare da nuna irin gudummawar UDUS ga ci gaban ilimi da zaman lafiya a Najeriya tun daga 1975 zuwa yau.
Jami’ar UDUS za ta karrama Sheikh Daurawa da digirin girmamawa
LEAVE A REPLY
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima

Wannan karramawa da Jami’ar UDUS za tayi wa Sheikh Daurawa gaskiya abin a yaba ne duma da irin Gudunmawar da yake bayarwa ta ko wane Bangare. Ubangiji Allah ya qaro mana Ilimi mai amfani