Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedJam'iyyar APC ta ce ba za ta bai wa Gwamnonin da suka...

Jam’iyyar APC ta ce ba za ta bai wa Gwamnonin da suka shiga jam’iyyar tikitin takara kai tsaye ba

Jam’iyyar APC ta bayyana cewa ba za ta bai wa gwamnonin da suka sauya sheƙa zuwa cikinta tikitin takarar kai tsaye ba a zabe mai zuwa.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa gwamnonin da ka iya rasa wannan dama dai akwai na Akwa Ibom, Umo Eno, Gwamnan Taraba, Agbu Kefas, Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, da kuma Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, wanda ake sa ran zai shiga a nan gaba.

Wani mamba na kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida cewa sauya sheƙa daga wata jam’iyya zuwa APC ba ya nufin samun tikiti kai tsaye.

Kazalika, daraktan yaɗa
Labarai na APC, Bala Ibrahim, ya tabbatar wa da jaridar ta Punch cewa jam’iyyar ta dimokuraɗiyya ce, kuma kowa zai bi tsarin yadda ake yin takara bisa ka’ida.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata