Wednesday, April 8, 2026
HomeBabban LabarinmuJam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kori Abdulmumini Jibrin Kofa

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta kori Abdulmumini Jibrin Kofa

Jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta sanar da kori ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa, bisa zargin ayyukan da suka saba wa jam’iyya da kuma kasa cika wajibin kuɗaɗen da ya rataya a wuyansa ga jam’iyyar.

Shugaban NNPP a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, wanda ya bayyana haka yayin jawabi ga manema labarai a Kano ranar Asabar, ya ce matakin ya biyo bayan kalaman da Jibrin ke yi a kafofin watsa labarai kan jam’iyyar da shugabanninta.

Daily Trust ta ruwaito cewa wannan lamari ya faru ne cikin sa’o’i 24 bayan ɗan majalisar ya bayyana cewa bai kamata a yi mamaki ba idan ya fice daga jam’iyyar.

Ya kuma ce ya isa girma don ya ɗauki matsaya da kansa kan abin da ya fi masa amfani a siyasance.

Da yake mayar da martani, Dungurawa ya bayyana Jibrin a matsayin “ɗan siyasa marar ƙarfi” wanda nasarar da ya samu a zaɓe ta faru ne kawai saboda goyon bayan tafiyar Kwankwasiyya da kuma jam’iyyar NNPP, ba wai ƙarfin kansa ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata