Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedJigon APC ya lakada wa kwamishina dukan tsiya

Jigon APC ya lakada wa kwamishina dukan tsiya

Shugaban jam’iyyar APC na wata mazaba a jihar Ondo Mr Olumide Awolumate ya yi bayani tiryan-tiryan dalilin da ya sa ya lakada wa kwamishinar mata da walwalar jama’a ta jihar dukan tsiya.
Ya ce sa’in-sa ce ta kaure tsakaninsu, da ta kai su ga dambacewa da Mrs Juliana Osadahun.
Bayanan da jaridar Punch ta tattara sun ce cacar bakin da ta kai ga kai dukan ta faru ne a wajen rabon kayan tallafin rage radadin tsadar rayuwa a karamar hukumar Arigidi Akoko ta jihar ta Ondo.
Bayanai sun ce jigon na APC Awolumate har ya raunata kwamishina Osadahun a kai. Sai dai rahotanni sun ce tuni uwar jam’iyya ta jiha ta dakatar da wannan shugaban jam’iyya na mazaba.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata