Tuesday, April 7, 2026
HomeBabban LabarinmuKakakin majalisar wakilai ya janye kudurin dokar tilasta wa 'yan Nijeriya yin...

Kakakin majalisar wakilai ya janye kudurin dokar tilasta wa ‘yan Nijeriya yin zabe

Kakakin majalisar wakilai Rt. Abbas Tajudeen, ya ce ya janye kudurin dokar tilasta wa kada kuri’a a lokacin zaben kasar, wanda ya dauki nauyin gabatarwa tare da dan majalisa Daniel Adama Ago.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Musa Abdullahi Krishi ya fitar a ranar Litinin, shugaban majalisar ya bayyana cewa, ya yanke shawarar janye kudirin yin gyara ga dokar zabe ta 2022.

A cewarsa, sun gabatar da kudirin ne da kyakkyawar niyya, domin karfafa huldar jama’a da kuma karfafa dimokuradiyyarmu ta hanyar karfafa masu kada kuri’a don su fito su yi zabe.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata