Kamfanin man fetur na kasa NNPCL ya sanar da rufe kamfanin tace man Fatakwal a hukumance.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, kamfanin na NNPC ya tabbatar wa da jaridar PUNCH cewa a ranar Asabar za a rufe kamfani na kimanin wata guda domin yin wasu gyararraki a kamfanin.
A cewar babban jami’in hulda da jama’a na kamfanin NNPC, Olufemi Soneye, za’a rufe ne a ranar Asabar 24 ga watan Mayu.
