Rahotanni daga jaridar Punch sun nuna cewa wasu daga cikin sabbin jakadun da Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada na iya fuskantar matsalar kin amincewa daga kasashen da aka tura su, sakamakon karancin lokacin wa’adin aikinsu.
Manyan jami’ai a Fadar Shugaban Kasa da kuma ma’aikatar harkokin diflomasiyya sun bayyana cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya na fuskantar kalubale wajen samun agrément — wato amincewar hukuma daga kasashen da za su karbi jakadun — ga wasu daga cikin wadanda aka zaba.
A cewarsu, wasu kasashe na bukatar jakada ya samu akalla wa’adin aiki na shekara daya ko biyu, wanda yawanci ake daura shi da tsawon wa’adin gwamnatin kasar da ta aike shi.
Tun da zaben shugaban kasa na gaba zai gudana a watan Fabrairun 2027, kuma wa’adin farko na Shugaba Tinubu zai kare a watan Mayun shekarar, jami’an sun bayyana damuwa cewa wasu kasashe ba za su so karbar jakadun da wa’adinsu ya yi kankanta ba a wannan lokaci.
Wani babban jami’in diflomasiyya da ya nemi a sakaya sunansa saboda muhimmancin batun ya ce:
“Babbar matsalar da muke fuskanta yanzu ita ce kasashe da dama, misali Indiya, na iya cewa idan wa’adin jakada bai kai shekara daya ko biyu ba, za su samu matsala wajen karbarsa. A yawancin lokuta, ana kallon wa’adin aiki har zuwa karshen gwamnatin da ke kan mulki.”
Kasashe na iya kin amincewa da sabbin jakadun Tinubu saboda karancin wa’adin aiki
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
