Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuKasashe na iya kin amincewa da sabbin jakadun Tinubu saboda karancin wa’adin...

Kasashe na iya kin amincewa da sabbin jakadun Tinubu saboda karancin wa’adin aiki

Rahotanni daga jaridar Punch sun nuna cewa wasu daga cikin sabbin jakadun da Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya nada na iya fuskantar matsalar kin amincewa daga kasashen da aka tura su, sakamakon karancin lokacin wa’adin aikinsu.

Manyan jami’ai a Fadar Shugaban Kasa da kuma ma’aikatar harkokin diflomasiyya sun bayyana cewa Ma’aikatar Harkokin Wajen Nijeriya na fuskantar kalubale wajen samun agrément — wato amincewar hukuma daga kasashen da za su karbi jakadun — ga wasu daga cikin wadanda aka zaba.

A cewarsu, wasu kasashe na bukatar jakada ya samu akalla wa’adin aiki na shekara daya ko biyu, wanda yawanci ake daura shi da tsawon wa’adin gwamnatin kasar da ta aike shi.

Tun da zaben shugaban kasa na gaba zai gudana a watan Fabrairun 2027, kuma wa’adin farko na Shugaba Tinubu zai kare a watan Mayun shekarar, jami’an sun bayyana damuwa cewa wasu kasashe ba za su so karbar jakadun da wa’adinsu ya yi kankanta ba a wannan lokaci.

Wani babban jami’in diflomasiyya da ya nemi a sakaya sunansa saboda muhimmancin batun ya ce:
“Babbar matsalar da muke fuskanta yanzu ita ce kasashe da dama, misali Indiya, na iya cewa idan wa’adin jakada bai kai shekara daya ko biyu ba, za su samu matsala wajen karbarsa. A yawancin lokuta, ana kallon wa’adin aiki har zuwa karshen gwamnatin da ke kan mulki.”

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata