DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Friday, April 10, 2026
HomeUncategorizedKiwon lafiyar mahajjatan Nijeriya zai kara inganta a hajjin 2025 -Hukumar NAHCON

Kiwon lafiyar mahajjatan Nijeriya zai kara inganta a hajjin 2025 -Hukumar NAHCON

Shugaban NAHCON tare da ministan lafiya

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta sha alwashin kara inganta shirin kiwon lafiya ga mahajjatan kasar a yayin aikin hajjin 2025 a kasar Saudiyya.
Ministan lafiya Farfesa Muhammad Ali Pate, ya sanar da hakan a lokacin da ya kammala duba kayan aikin kiwon lafiya a sashen Hukumar Kula da aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON a birnin Makkah, Saudiya.
A lokacin ziyarar da ya kai ofishin NAHCON da ke Ummul-Jud a Makkah, Minista Pate ya tabbatar da cikakken goyon bayan gwamnati domin magance manyan matsalolin kiwon lafiya da mahajjatan Nijeriya ke fuskanta.  
A cikin wata sanarwa da Muhammad Ahmad Musa, jagoran sashen yada labaran NAHCON ya fitar, hukumar ta shirya aikin hajji a Nijeriya ta ce minista Ali Pate tare da rakiyar manyan jami’an ma’aikatar lafiya, ya gudanar da cikakken bincike kan motocin daukar marasa lafiya na NAHCON, duba kayayyakin likitanci, da kuma tantance shirin kayan aikin asibitocin Nijeriya a Saudiyya.
Minista Mohammed Ali Pate tare da shugaban NAHCON Farfesa Saleh Pakistan a Makkah

Ziyarar ta haskaka muhimman fannoni da ke bukatar ingantawa, ciki har da karin magungunan da ake bukata, rigakafi, kayan aikin likitanci, da kuma motocin daukar marasa lafiya da za su iya aiki yadda ya kamata.
Shugaban hukumar kula da Aikin Hajji ta NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya yaba da shirin Ministan, yana mai jaddada muhimmancinsa musamman ga kula da lafiyar alhazan Nijeriya.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata