Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedKotu ta dage sauraron ƙarar da gwamnatin kano ta shigar kan sarautar...

Kotu ta dage sauraron ƙarar da gwamnatin kano ta shigar kan sarautar Kano

Kotu ta dage sauraron ƙarar da gwamnatin kano ta shigar kan sarautar Kano

wata babbar kotu a jihar Kano ta dage ci gaba da zamanta har zuwa ranar 4 ga watan Yuli, inda za ta ci gaba da sauraren karar da gwamnatin Kano ta shigar tana bukatar tabbatar Sarki Sunusi na biyu a kejerar sarauta.

Babban lauyan gwamnatin jihar Kano da majalisar dokokin jihar ta bakin Lauyan su Ibrahim Isah-Wangida suka shigar da karar a ranar 27 ga watan Mayu.

Suna neman a bada umarnin hana Sarkin Kano na 15, Aminu Ado-Bayero da wasu sarakuna hudu da aka tube daga sarautar Bichi, Rano, Gaya da Karaye bayyana kansu a matsayin sarakunan gargajiya.

Sauran wadanda aka yi ƙarar su sun hada da Sufeto-Janar na ’Yan sanda, Daraktan jami’an tsaro na farin kaya a Jiha, da jami’an tsaro na Civil Defence da Sojojin Nijeriya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata