Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince hukumar EFCC ta ci gaba da tsare tsohon Ministan Shari’a kuma Lauyan Gwamnatin Tarayya, Abubakar Malami (SAN).
Mai shari’a Babangida Hassan ya yi watsi da bukatar beli da Malami ya shigar, yana mai cewa tsarewar na gudana ne bisa sahihin umarnin da wata kotu mai matsayi ta daya ta bayar a baya.
A cewar sanarwar da kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya fitar, lauyan Malami ya yi ikirarin cewa an tsare Malami ba bisa ka’ida ba, amma lauyan EFCC ya shaida wa kotu cewa Mai shari’a S. C. Oriji ya bayar da umurnin hakan kamar yadda dokar ACJA ta tanada.
Rahotanni sun ce Malami na tsare tun ranar 8 ga Disamba bayan ya kasa cika sharuddan beli da EFCC ta gindaya, yayin da ake bincikensa kan zarge-zarge 18 da suka hada da cin zarafin ofis da zargin tallafa wa ta’addanci.
