Sunday, April 5, 2026
HomeBabban LabarinmuKotu za ta yanke hukunci kan belin Abubakar Malami a ranar 7...

Kotu za ta yanke hukunci kan belin Abubakar Malami a ranar 7 ga Janairu

Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta sanya 7 ga Janairu domin yanke hukunci kan bukatar beli da Abubakar Malami, tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, ya gabatar bisa zargin safarar kudi.

A halin yanzu, Malami na tsare a gidan gyara hali na Kuje tare da dansa, Abdulaziz Malami, da daya daga cikin matansa, Bashir Asabe, wadanda ke fuskantar shari’a a gaban kotu.

Hukumar EFCC ta shigar da tuhume-tuhume 16 a kansu, tana zarginsu da safarar kudade har Naira biliyan 8.7. Dukkaninsu sun musanta zargin lokacin da aka gurfanar da su a ranar 29 ga Disambar 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata