Kotun Kolin Nijeriya ta umurci gwamnatin Tinubu ta aiwatar da umurnin bai wa kananan hukumomin kudadensu kai tsaye
Kotun ta nuna damuwarta kan yadda Gwamnatin Tarayya ta kasa aiwatar da hukuncin da ta yanke a Yuli 2024 cewa a rika biyan kuɗaɗen ma’aikatar tarayya na kananan hukumomi kai tsaye zuwa gare su, ba tare da tsoma bakin jihohi ba.
Rahoton jaridar Punch ya ce hukuncin da Alkalin Kotun Koli Justice Mohammed Idris ya karanta jiya, kotun ta ce babu wata hujja mai kwair da ke nuna cewa Ministan Shari’a na Tarayya (AGF) ya ɗauki matakan da suka dace domin cika wannan hukuncin.
Kotun ta umarci gwamnati da ta gaggauta farawa aiwatar da hukuncin.
