Kungiyar kare hakkin jama’a da tabbatar da gaskiya a harkokin gwamnati (SERAP) ta shigar da ƙara a kotu kan Hukumar Rabon Kuɗaɗe da Tsare-Tsaren Kuɗin Gwamnati (RMAFC) bisa shirin ƙara wa manyan jami’an gwamnati albashi, ciki har da shugaban ƙasa, mataimakin shugaban ƙasa, gwamnoni da mataimakansu, da kuma ’yan majalisa.
A watan da ya gabata, RMAFC ta bayyana cewa ta na da shirin ƙara wa shugabannin ƙasa da gwamnoni da ’yan majalisa albashi, inda ta ce albashin da ake biyansu a yanzu “kaɗan ne.”
Sai dai a wata sanarwa da mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya fitar a ranar Lahadi, ya tabbatar da cewa sun maka hukumar a kotu, duk da cewa har yanzu ba a saka ranar sauraren ƙarar ba.
A ƙarar da aka shigar a makon da ya gabata a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, mai lamba FHC/ABJ/CS/1834/2025, SERAP ta nemi kotu ta tantance ko shirin ƙarin albashin shugaban ƙasa, mataimakinsa, gwamnoni da mataimakansu, da kuma ’yan majalisa bai sabawa doka, kundin tsarin mulki da kuma dokokin RMAFC ba.
Kungiyar ta roƙi kotu ta ayyana cewa shirin ƙarin albashin ya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) da dokar RMAFC, don haka ya kasance ba bisa ka’ida ba.
Kungiyar SERAP ta maka hukumar RMAFC kotu kan shirin ƙara albashin Tinubu da gwamnoni
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
