Wednesday, April 8, 2026
HomeUncategorizedKwankwaso da ɗarikar sa ta Kwankwasiyya barazana ce ga jam’iyyar NNPP -...

Kwankwaso da ɗarikar sa ta Kwankwasiyya barazana ce ga jam’iyyar NNPP – Shugaban tsagin jam’iyyar na kasa Dr. Gilbert Agbo

Shugaban tsagen jam’iyyar NNPP na kasa Dr. Gilbert Agbo wanda ya jagoranci gangamin adawa da Kwankwasiyya a sakatariyar jam’iyyar a Minna jihar Neja, ya ce Kwankwaso da tawagar sa ta Kwankwasiyya barazana ce ga ci gaba da wanzuwar jam’iyyar.

Da yake jawabi a wurin taron shiyyar Arewa ta tsakiya a Minna, Dr. Agbo ya jaddada cewa dakatarwar da jam’iyyar ta yiwa Kwankwaso a Legas ya kawo karshen zama mamba da hannun a jam’iyyar nan take.

Dr. Gilbert wanda shi ma ya jagoranci kona jar hular ta kungiyar Kwankwasiyya a sakatariyar jam’iyyar ta jihar a Minna, ya ce matakin ya nuna karara na ballewa daga bangaren Kwankwaso.

Dokta Agbo ya ce ana sa ran gwamna Kabir Yusuf na jihar Kano zai gurfana a gaban kwamitin ladabtarwar jam’iyyar saboda rashin bin ka’idojin jam’iyyar da kuma daukakar jam’iyyar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata