Magoya bayan Sarkin Kano Aminu Ado Bayero, da na Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, sun yi arangama a ranar Lahadi a harabar fadar Kofar Kudu, yayin da Aminu Bayero ke dawowa daga gidan sa da ke Mandawari.
Rahotanni sun bayyana cewa a yayin arangamar, an fasa kofar fadar, tare da farma masu gadin fada har wasu suka ji rauni, sannan an lalata motoci na ‘yan sanda da ke cikin harabar fadar, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A cikin wata sanarwa da sashen yada labarai na Masarautar Kano ya fitar, wadda Sadam Yakasai ya rattaba wa hannu, ta zargi magoya bayan Aminu Ado Bayero da haddasa rikici a lokacin da Sarki Muhammadu Sanusi II bai nan.
Kokarin samun martani daga bangaren Sarki Aminu Ado Bayero ya ci tura, domin mai magana da yawunsa, Abubakar Kofar-Naisa, bai dauki kiran waya da jaridar ta yi masa ba.
Sai dai Muktar Dahiru, daya daga cikin masu rakiya tare da Bayero kuma wanda ya shaida faruwar lamarin, ya karyata zargin da Sadam Yakasai ya yi.
Magoya bayan Sarki Aminu Bayero da na Sarki Muhammadu Sanusi sun yi rikici a fadar Kofar Kudu
RELATED ARTICLES
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
