Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedMajalisar Dattawan Nijeriya za tayi doka kan albashin jami'an shari'ar a kasar.

Majalisar Dattawan Nijeriya za tayi doka kan albashin jami’an shari’ar a kasar.

Majalisar Dattawan Nijeriya za tayi doka kan daidaita albashin jami’an shari’a na tarayya da na jihohi.

Majalisar dattijai ta yi zaman karatu na biyu, kan kudirin dokar da za ta tsara albashi, da alawus-alawus da na ma’aikatan shari’a a Nijeriya.

Kudurin wanda dan majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele ya gabatar, wanda yasamu  karatu na biyu biyo bayan muhawarar da sanatocin suka gabatar a zauren majalisar.

A yayin muhawarar , Bamidele ya bayyana cewa, kudirin doka ce ta zartarwa, wanda shugaba Bola Tinubu ya mikawa majalisun tarayyar guda biyu, bisa tanadin sashe na 58 (2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999, kamar yadda aka gyara.

A cewar sa, daya daga cikin kudirorin dokar shine hada kan tsarin albashi da alawus-alawus na masu rike da mukaman shari’a a matakin tarayya da jihohi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata