Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMajalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai a jihar Kebbi da DCL Hausa ta yi rahoton zargin da ake yi masa na cefanar da fili da ‘transatomomi’.

Majalisar Dokokin Jihar Kebbi ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Fakai, Muhammad Mahuta, bisa zargin aikata munanan ayyuka da sakaci wajen gudanar da aikinsa, biyo bayan amincewa da rahoton kwamiti na musamman da majalisar ta kafa ƙarƙashin jagorancin Salihu Dangoje, kamar yadda rahoton jaridar Punch ya nuna.

A cewar kwamitin, bincike ya gano zarge-zargen haɗa hannu wajen cire da kuma yunƙurin sayar da injinan wuta guda biyar, rabon gonakin gwamnati ba bisa ka’ida ba, da karya yarjejeniyar aikin gyaran madatsar Mahuta.

Kwamitin ya ce Mahuta ya bayyana musu cewa an ɗauki injinan ne domin gyara da izinin wani jami’in KEDCO mai suna Malam Nasir, wanda bai amsa gayyatar kwamitin ba.

Sai dai a ranar 14 ga Nuwamba, shugaban ƙaramar hukumar ya amsa gaban kwamitin cewa ya yi almundahanar injinan guda biyar da ake shirin sayar wa wani Alhaji Kabiru Dauda kan naira miliyan 2.5 kowanne.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata