Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedMajalisar Dokokin Kano ta musanta yunkurin tsige mataimakin gwamna

Majalisar Dokokin Kano ta musanta yunkurin tsige mataimakin gwamna

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta karyata rahotannin da ke yawo na cewa ana shirin tsige Mataimakin Gwamnan jihar, Alhaji Aminu Abdulsalam Gwarzo, tana mai bayyana rahotannin a matsayin marasa tushe.

Da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Asabar, mai magana da yawun Kakakin Majalisar, Kamaluddeen Sani Shawai, ya ce babu wata tattaunawa, kudiri ko shiri a cikin Majalisar da ke nufin tsige mataimakin gwamnan.

Ya jaddada cewa rahotannin da wasu kafafen yada labarai ke yadawa ba su da sahihanci, kuma na iya haddasa tashin hankali na siyasa ba tare da wani dalili ba a jihar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata