Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedMajalisar wakilai za tai binciken kan abinda ke tsakanin matatar man Dangote...

Majalisar wakilai za tai binciken kan abinda ke tsakanin matatar man Dangote da hukuma kula da man fetur ta Nijeriya

Majalisar wakilai za tai binciken kan abinda ke tsakanin matatar man Dangote da hukuma kula da man fetur ta Nijeriya

Majalisar takilai ta ce za ta binciki cece-ku-cen da ke faruwa tsakanin matatar mai ta Dangote da hukumar hula da man fetur ta Nijeriya (NMDPRA).

Haka kuma binciken zai hada da hukumar kula da man fetur ta Nijeriya (NUPRC) da Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL).

Mataimakin mai magana da yawun majalisar wakilai, Philip Agbese ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Asabar.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN) ya rawaito cewa binciken na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da matsalar karancin mai a fadin kasar da kuma zargin cewa man Dangote ba shi da inganci.

Agbese ya ce binciken ya yi daidai da kudurin majalisar na kare dukkan kadarorin kasa da muhimman ababen more rayuwa na tattalin arziki kamar matatar man Dangote.

Ya ce: “Mun dade muna gani ta hanyar yin kamfen don bata sunan matatar man Dangote da kuma la’akari da mummunan tasirin da hakan ya haifar da firgici a kasar.

Yace abin takaici, abin da muka gani shi ne, NNPC da NMDPRA na taka rawar gani sosai a cikin wadannan makirce-makircen don bata sunan matatar, wanda kuma ba za a amince da shi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata