Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuMajalisar dokoki ta nemi a fallasa masu daukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Majalisar dokoki ta nemi a fallasa masu daukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Majalisar dokokin Nijeriya ta bukaci gwamnatin ƙasar ta bayyana sunayen mutanen da ke daukar nauyin ta’addanci tare da gurfanar da su a gaban kotu.

 

Wannan kira daga majalisar dattawa da ta wakilai, ya zo a daidai lokacin da gwamnati ta bayyana cewa ta fara daukar matakai don magance ta’azzarar matsalar a sassa daban daban na kasar, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

 

A hannu guda, majalisar dattawa ta kuma bukaci a rika zartarwa da masu garkuwa da mutane hukuncin kisa, da kuma duk wanda ke daukar nauyinsu, ko yake taimaka musu da bayanai, yayin da ‘yan majalisar ke tattaunawa kan gyaran dokar hana ta’addanci ta shekarar 2022.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata