Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMinistar Kwadago a gwamnatin Tinubu ta yi murabus daga mukaminta

Ministar Kwadago a gwamnatin Tinubu ta yi murabus daga mukaminta

Nkeiruka Onyejeocha ta yi murabus daga muƙaminta na Karamar Ministar Kwadago da Ayyuka domin shirin takarar zaɓen 2027.

Ta zama ta uku cikin ministocin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da suka ajiye aiki, bayan umarnin shugaban Nijeriya ga masu niyyar tsayawa takara su sauka kafin ƙarshen Maris.

Ta sanar da murabus ɗin nata ne ta cikin wata wasiƙa da ta wallafa a shafukan sada zumunta, amma ba ta bayyana kujerar da take shirin nema ba.

Ministar ta gode wa shugaban Nijeriya da ma’aikatan ma’aikatar bisa haɗin kai, tana mai cewa za ta ci gaba da hidimtawa ƙasa a wani sabon mataki.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata