Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na samar da isasshen kudade ga muhimman bangarorin bunkasa tattalin arzikin kasa, domin kyautata rayuwar ‘yan Nijeriya.
Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a wajen bude taron kasa kan asusun jama’a da tsarin kashe kudade, wanda kwamitocin kula da kudade da al’umma na Majalisar Dattawa da ta Wakilai suka shirya.
Da take wakiltar shugaban kasa, karamar ministar kudi Doris Uzoka-Anite, ta ce cire tallafin man fetur, duk da cewa abi ne mai radadi amma ya bai wa gwamnati damar karkata kudaden zuwa inganta sufuri, kafa sabbin tsare-tsaren jin kai, da kuma gina muhimman ababen more rayuwa da za su amfani ‘yan Nijeriya.
