Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaMuna kira ga ‘yan Nijeriya kar su sake zabar Tinubu saboda gazawa...

Muna kira ga ‘yan Nijeriya kar su sake zabar Tinubu saboda gazawa wajen samar da wutar lantarki – Peter Obi 

Tsohon ɗan takarar shugabancin Nijeriya a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bukaci ‘yan kasar kada su sake zaɓen Shugaba Tinubu, yana mai danganta hakan da gazawa wajen inganta wutar lantarki a ƙasar.

Obi ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya tuna cewa Tinubu ya yi alkawarin idan bai samar da wutar lantarki mai dorewa cikin shekaru huɗu ba, kada a sake zaɓensa.

Ya ce a halin yanzu alkawarin bai cika ba saboda samun wutar lantarki ya ragu daga sama da megawatt 4,000 a shekarar 2023 zuwa ƙasa da haka yanzu, yayin da kuma farashin lantarki ke karuwa sossai.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata