Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedMutane 25 ne suka rasa rayukansu, yayinda da 53 suka jikkata a...

Mutane 25 ne suka rasa rayukansu, yayinda da 53 suka jikkata a wani hadarin mota a Kano

Mutane 25 ne suka rasa rayukansu, yayinda da 53 suka jikkata a wani hadarin mota a Kano

Hukumar kiyaye afkuwar haddura ta kasa reshen jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar matafiya 25, yayin da wasu 53 suka samu raunuka a wani hatsarin mota.

Hatsarin ya afku ne da sanyin safiyar Litinin a kusa da Kasuwar Dangwaro, dake hanyar zariya a Kano.

Matafiyan sun yi lodi ne a cikin wata tirela wadda take dauke da shanu ta da zata tafi yankin kudancin Nijeriya daga Maiduguri.

A cewar kwamandan hukumar FRSC a jihar, Ibrahim Abdullahi, hatsarin ya afku ne da wata tirela (IVECO) mai lamba XA 311 ZB.

Yace an kira su ne da misalin karfe 03:15 na daren ranar 1 ga Yuli, 2024. Da samun labarin, suka yi gaggawar aika jami’ai da motar  zuwa inda lamarin ya faru domin ceto wadanda lamarin ya shafa da karfe 03:30.

Kwamandan sashin ya ce hatsarin ya afku ne sakamakon gudun wuce gona da iri da motocin keyi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata