Tuesday, April 7, 2026
HomeBabban LabarinmuMutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka...

Mutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka biya kudin fansa, aka karbi kudin aka kuma ki sako mutanen a jihar Kaduna

Dattawan al’ummar Gidan Waya da ke ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna sun bayyana cewa sun sayar da buhunan masara sama da 3,000 domin tara Naira miliyan 40 da masu garkuwa da mutane suka nema a matsayin kudin fansa, amma duk da biyan kudin, mutane 13 da aka sace har yanzu na ci gaba da zama a hannun masu garkuwa bayan shafe makonni.

Da yake magana a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Litinin, Shugaban Kwamitin Dattawa, Malam Rabo Sambo, ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun kai hari al’ummar Gidan Waya ne da tsakar dare a ranar 11 ga Nuwamba, 2025, inda suka kashe mutane hudu, sannan suka yi garkuwa da mutane 13 da suka hada da maza biyar da mata takwas.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata