Sunday, April 5, 2026
HomeUncategorizedNa yi matuƙar farin ciki da hukuncin kotun ƙoli kan yancin ƙananan...

Na yi matuƙar farin ciki da hukuncin kotun ƙoli kan yancin ƙananan hukumomi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar kuma madagun adawa a Kasar ya yaba hukuncin kotun koli da ya baiwa kananan hukumomin ƙasar ikon sarrafa kuɗaɗen su ba tare da an hada su da gwamnoni ba.

Atiku, a shafin sa na twitter, ya ce wannan mataki na kotun ƙoli nasara ce ga yan Najeriya kuma abin a yaba ne matuka saboda ya kawar da mummunan tsarin nan da gwamnatocin jihohi ke amfani da shi suna sakaye kuɗaɗen ƙananan hukumomi a asusun gwamnatin jiha.

Madugun adawan na Najeriya yayi fatan yancin na kananan hukumomi zai zarta ɓangaren kudi kadai, yana bayar da shawarar a raba su da jihohi kuma wurin karbar Barack da tara shi saboda yadda ya ce gwamnatocin jihohi ke yin yadda suka ga dama da kuɗin haraji na kananan hukumomi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata