Tuesday, April 7, 2026
HomeUncategorizedNAHCON ta aike da ma‘aikatan farko da za su tarbi maniyyata zuwa...

NAHCON ta aike da ma‘aikatan farko da za su tarbi maniyyata zuwa Saudiyya

Tawagar ma’aikata 43 daga hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON za su tashi daga Abuja a gobe Lahadi, zuwa kasar Saudiyya, domin murnar tarbar jirgin farko na mahajjatan Nijeriya a kasar Saudiyya.
Tawagar da ta kunshi jami’an hukumar NAHCON 35 da ma’aikatan lafiya 8 za su je kasar Saudiyya domin shirin karshe na karbar mahajjatan Nijeriya daga jihar Kebbi da za su isa Saudiyya a ranar Laraba 15 ga watan Mayu domin gudanar da aikin Hajjin bana na shekarar 2024.
Da yake jawabi ga tawagar a wani dan takaitaccen biki na ban kwana da aka gudanar a dakin taro na hukumar, Abuja, shugaban hukumar Malam Jalal Ahmad Arabi ya gargadin cewa hukumar za ta dauki tsattsauran mataki a kan duk wanda aka samu rahoton ya kauce wa ka’idar aiki ga amanar da aka dora musu.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata