Monday, April 6, 2026
HomeUncategorizedNi zan yi nasarar lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027 -...

Ni zan yi nasarar lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027 – Kwankwaso

 Ni zan yi nasarar lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2027 – Kwankwaso

Babban jigo a jam’iyyar NNPP a Nijeriya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce shi ne zai yi nasarar lashe zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Kwankwaso, wanda shi ne ya yi wa jam’iyyar ta NNPP takarar shugaban kasa a zaben 2023, kuma shi ne ya zo na hudu a zaben, ya yi wannan furuci ne a ranar Asabar a lokacin da ya kaddamar da sakatariyar jam’iyyar NNPP, a kan titin IBB, a jihar Katsina.

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya ce Kwankwaso ya isa jihar Katsina ne domin yin ta’aziyyar rasuwar Hajiya Dada mahaifiyar tsohon shugaban Nijeriya Marigayi Umaru Musa ‘Yar’Adua. 

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata