Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuNijar da Nijeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro da farfado da...

Nijar da Nijeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro da farfado da kasuwanci a iyakar kasashen

Daraktan Janar na Hukumar Kwastam na Nijar, Colonel Mohamed Siddo Yacouba, ya kai ziyarar aiki a Abuja inda ya tattauna da takwaransa na Hukumar Kwastam ta Nijeriya.

Bayan wani zama tsakanin wakilan ƙasashen biyu, an rattaba hannu kan yarjejeniyoyi don ƙarfafa tsaro a iyakar kasashen don sauƙaƙe da farfado da harkokin kasuwanci a manyan hanyoyin shiga da fita tsakanin kasashen.

Wannan mataki na nuna fara sasantawa tsakanin mahukuntan Abuja da Niamey bayan watanni na rikicin diflomasiyya tsakanin kasashen makwabta.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata