Tuesday, April 7, 2026
HomeSiyasaNijeriya ce ta taimaka wa Benin ta dakile yunkurin juyin Mulki -...

Nijeriya ce ta taimaka wa Benin ta dakile yunkurin juyin Mulki – Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Nijeriya ce ta taimaka wa Jamhuriyar Benin wajen dakile yunkurin juyin mulki da wasu sojojin ƙasar suka yi.

A cikin sanarwar da fadar shugaban kasa ta rabawa manema labarai ciki har da DCL Hausa, Tinubu ya jinjina wa sojojin saman Nijeriya da suka hanzarta tashi zuwa Benin domin kawo dauki, tare da tabbatar da cewa dakarun kasa ma sun isa can don tabbatar da ganin an kare tsarin dimokuraɗiyyar ƙasar.

Tinubu ya ce gwamnatin kasar ta Benin ce ta nemi taimako, kuma ya amince da gaggawa domin kare su daga sojojin da suka yi yunkurin karya tsarin mulkin farar hula a kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata