Monday, April 6, 2026
HomeBabban LabarinmuObasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima -...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Tinubu Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya ce tasirin Obasanjo a Nijeriya Afirka da ma duniya baki ɗaya yana da girma sosai.

Shugaban ya jaddada cewa Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa ƙasa hidima, inda ya taba zama shugaban mulkin soja daga shekarar 1976 zuwa 1979, kafin ya miƙa mulki ga gwamnatin farar hula a 1979.

Haka kuma ya sake zama shugaban ƙasa na farar hula a jamhuriya ta huɗu daga 1999 zuwa 2007.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata