Tuesday, April 7, 2026
Home Blog Page 26

Majalisar dattawan Nijeriya ta kira zaman gaggawa kan cece-kucen gyaran dokar zabe

0

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta gudanar da zaman gaggawa a yau Talata, sakamakon karuwar muhawara da zanga-zanga kan gyaran Dokar Zabe, musamman batun tura sakamakon zabe ta yanar gizo.

Sanarwar zaman ta fito ne a cikin wata takarda da Magatakardar Majalisar, Emmanuel Odo, ya fitar bisa umarnin Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio.

Muhawarar ta fi karkata ne kan Sashe na 60, Karamin Sashe na 3, wanda ya shafi tura sakamakon zabe ta yanar gizo.

Majalisar ta ki amincewa da kudurin da zai wajabta tura sakamakon zabe kai tsaye a lokaci guda, inda ta bar tanadin da ke cikin Dokar Zabe ta 2022.

Tanadin da aka bari na cewa jami’in rumfar zabe zai tura sakamakon, ciki har da adadin masu kada kuri’a, ta hanyar da Hukumar Zabe (INEC) za ta tanada.

Kudurin da aka ki amincewa da shi kuwa ya bukaci a rika tura sakamakon rumfar zabe kai tsaye zuwa dandalin IREV bayan kammala sa hannu da hatimi kan takardun sakamako.

Naira 36m kacal aka saki daga ₦218bn na kasafin lafiya – Ministan Lafiya

0

Ministan Lafiya na Nijeriya, Farfesa Mohammed Ali Pate, ya bayyana cewa ma’aikatarsa ba ta iya aiwatar da kasafin ci gaban lafiya na shekarar 2025 ba, sakamakon sakin ₦36 miliyan kacal daga cikin ₦218 biliyan da aka ware wa bangaren.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin zaman kare kasafin kudin 2026 a gaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Harkokin Kula da Lafiya.

Ya ce duk da cewa an saki kasafin albashi gaba ɗaya, bangaren kasafin manyan aiyuka bai samu isasshen kudi ba, lamarin da ya danganta da tsarin tsara sakin kudi daga kasa zuwa sama da ofishin Akanta Janar na Tarayya ke amfani da shi.

Jaridar Daily Trust ta ambato Farfesa Pate ya kuma shaida wa ‘yan majalisar cewa ma’aikatar ta kasa samun wasu kudaden hadin gwiwa saboda jinkirin sakin gudunmuwar Nijeriya, wanda hakan ya janyo tsaiko wajen aiwatar da kasafinta na 2025.

Nijeriya ce kasa ta 36 a jerin kasashen da suka fi cin hanci a duniya – Bincike

Kungiyar Transparency International (TI) ta sake sanya Nijeriya a matsayi na 36 cikin kasashen da suka fi cin hanci a duniya a shekarar 2025, a cewar rahoton Corruption Perceptions Index (CPI) da aka fitar ranar Talata.

Rahoton ya nuna cewa Nijeriya ta fadi daga matsayi na 140 a 2024 zuwa 142 cikin kasashe 182 da aka tantance, inda maki 0 ke nuna mafi muni wajen cin hanci, yayin da 100 ke nuni da mafi tsabta.

Nijeriya ta samu makin 26, inda ta yi kunnen doki da kasashe irin su Cameroon, Guatemala, Guinea, Kyrgyzstan da Papua New Guinea.

Duk da faduwar matsayin, Nijeriya ta ci gaba da kasancewa a matsayin kasa ta 36 mafi cin hanci, kamar yadda ta kasance a shekarar da ta gabata.

Shugaba Tinubu ya sasanta rikicin Wike da Fubara a Abuja

0

Shugaba Bola Tinubu ya shiga tsakani wajen sasanta rikicin siyasa a jihar Rivers, inda suka gana da Gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da Ministan Abuja Nyesom Wike, a fadar shugaban kasa, a daren Litinin.

Jaridar The Nation, ta ruwaito cewa Shugaba Tinubu ya gana da shugabannin jihar Rivers ciki har da Wike da Fubara, tare da wasu shugabannin siyasa daga jihar.

Rahotanni sun bayyana cewa Fubara ya yi alkawarin nuna girmamawa ga Wike a nan gaba, alamar cewa rikicin siyasa tsakanin manyan ‘yan siyasar jihar na iya samun sassauci.

Hare-hare kan ofisoshin ‘yan sanda ya yi sanadin halaka jami’an ‘yan sanda 45 a cikin shekara guda – Daily Trust

0

Wani rahoto ya bayyana cewa halin tsaro a Nijeriya ya ƙara tabarbarewa a cikin shekara guda da ta gabata, sakamakon hare-hare da aka rika kai wa ofisoshin ‘yan sanda, wuraren bincike a jihohi daban-daban na ƙasar.

Wadannan hare-hare sun yi sanadin halaka jami’an ‘yan sanda da dama, inda aka kona ofisoshi, aka kwace makamai, aka saki wadanda ake tsare da su.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa akalla jami’an ‘yan sanda 45 ne suka rasa rayukansu a cikin shekara guda sakamakon hare-hare kan ofisoshin ‘yan sanda, wuraren bincike da a jihohi da dama ciki har da Borno, Kwara, Enugu, Kano, Jigawa, Bauchi, Plateau, Kogi, Taraba, Benue, Zamfara, Niger, Edo, Kaduna da Oyo.

Gwamnan Bauchi Bala ya sauke kwamishina tsaron cikin gida na jihar

0

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya sallami Kwamishinan tsaron cikin gida da na jihar, Alhaji Ibrahim Gambo Galadima, daga mukaminsa.

Jaridar Punch ta rawaito cewa sanarwar sallamar ta fito ne ta bakin mai bai wa Gwamnan shawara kan harkokin yada labarai, Mukhtar Gidado, wanda ya bayyana cewa matakin na cikin sauyin da aka yi a Majalisar zartarwar jihar domin sake tsarawa da ƙarfafa aikin gwamnati.

A cewar sanarwar, sauyin na da nufin kawo sabbin dabaru, da tsarin shugabanci, da kuma inganta aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati a fadin jihar.

Duk wanda ke goyon bayan cin amana shima za a ci amanarsa Wike ga Gwamnonin da ke goyon bayan Sim Fubara

0

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya gargadi gwamnonin da sauran ’yan siyasa da ke goyon bayan Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, cewa goyon bayan “cin amana” zai koma musu.

Wike ya bayyana haka ne yayinda yake jawabi wajen taro ranar Asabar a birnin Fatakwal na jihar Rivers, ya ce duk wanda ke mara wa mai cin amana baya, shi ma za a ci amanarsa a nan gaba.

Rikicin Wike da Fubara ya samo asali ne daga takaddamar a siyasar Rivers, duk da ƙoƙarin sulhu da aka yi, har zuwa wannan lokaci rikicin na ci gaba da shafar harkokin siyasa a jihar.

NLC ta yi barazanar zanga-zanga kan “ruɗani” kan dokar zaɓe da majalisa ke gyara

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi gargaɗin yiwuwar zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da kuma kaurace wa zaɓe, sakamakon abin da ta kira ruɗani da saɓanin matsaya daga Majalisar Dattawa kan gyaran Dokar Zaɓe, musamman game da aika sakamakon zaɓe ta na’ura.

Kungiyar ta zargi Majalisar Dattawa da watsi da buƙatar jama’a ga tsarin zaɓe a Nijeriya, saboda kasa fayyace ko aika sakamakon zaɓe ta na’ura tilas ne ko a’a.

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, inda ya ce kungiyar na nuna damuwa mai tsanani kan “ruɗani da bayanai masu karo da juna” da ke fitowa daga Majalisar Dattawa dangane da gyaran Dokar Zaɓe ta 2022, musamman a kan batun e-transmission.

Akpabio ya caccaki masu sukar aikin gyaran Dokar Zaɓe da majalisar dattawa ke yi

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya kare matakin Majalisar kan gyaran Dokar Zaɓe, yana mai cewa masu sukar aikin na yanke hukunci ne tun kafin kammala bin tsarin dokar.

Akpabio ya jaddada cewa Majalisar ba ta cire tsarin aika sakamakon zaɓe ta na’ura daga dokar ba, sai dai ta ɗora ayar tambaya kan sharadin aika sakamakon a lokacin da ake yin zaɓe.

A cewar wata sanarwa da jaridar Punch ta ruwaito, Akpabio ya yi wannan bayani ne a Abuja yayin da ya halarci bikin kaddamar da littafin The Burden of Legislators in Nigeria na Sanata Effiong Bob, inda ya kasance bako na musamman.

Hukumar CAC ta soke kamfanoni sama da 400,000 da ba sa aiki

Hukumar Rajistar Kamfanoni ta Nijeriya (CAC) ta bayyana cewa ta soke rajistar kamfanoni sama da 400,000 da ba sa aiki daga kundin rajistar kamfanoni a shekarar 2025, a matsayin wani bangare na sauye-sauyen da ake yi domin inganta gaskiya, kare tattalin arziki, da dawo da amincewar masu zuba jari.

Babban Darakta na CAC, Hussaini Magaji, SAN, ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a Abuja yayin tattakin motsa jiki na wata-wata da hukumar ta shirya, cikin ayyukan bikin cikar CAC shekaru 35 da kafuwa.

Magaji ya ce yawancin kamfanonin da abin ya shafa sun dade ba sa mika rahotannin shekara-shekara na doka, kuma ba sa gudanar da wani aiki, yana mai gargadi cewa irin wadannan kamfanoni na iya jefa tattalin arziki cikin hadari.