Talauci zai karu idan aka dawo da tallafin mai a Nijeriya – Shugaban NOA
Dokar shigo da kayan abinci ba tare da biyan haraji ba, za ta fara aiki mako mai kamawa – FG
APC ta karbi tubar Ali Ndume ta kuma yafe masa
Babban bankin kasar Kenya ya rage kudin ruwa
‘Yan siyasar da suka sha kaye a zaben 2023 ne ke ruruta zanga-zanga a Nijeriya – Zargin matasan APC
Da ba a shafa wa Yahaya Bello da El-rufa’i kashin kaji ba, da sun tausashi zukatan masu zanga-zanga a arewa – Jigon APC
Akwai bukatar Sanata Akpabio ya sauka daga mukaminsa – Jigon APC
Jami’anmu ba su yi harbi da harsashi mai rai ba a lokacin zanga-zanga – IGP
Jami’anmu ba su yi harbi a lokacin zanga-zanga ba – IGP
Babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun ya ce babu jami’insu da ya yi harbi a lokacin zanga-zanga.
Sufeton ya bayyana haka ne a lokacin ya ke jawabi a taron shugabanin tsaro a ranar Talatar,a Abuja lokacin da yake kare zargin da aka yi wa jami’ansu na yin harbi a yayin zanga-zangar matsin rayuwa da aka yi a Nijeriya.
Ya ce duk jami’in da aka gani da bakin kaya a ranar zanga-zanga ba jami’insu ba ne saboda ba kayan da suka saba sanyawa suka sa ba a ranar.
Sannan ya ce,sun kama masu dinka tutocin kasashen waje don su kai su wajen masu daukar nauyinsu.
Ko a jihar Kano ‘yan sanda sun fara gurfanar da wa’yanda ake zargi da tayar da tarzoma tare da bannata dukiyoyin al’umma a yayin zanga -zangar.
Mun shirya biyan N70,000 mafi karancin albashi – Gwamnatin jihar Nasarawa
Mun shirya biyan N70,000 mafi karancin albashi – Gwamnatin jihar Nasarawa
Dakatar da biyan harajin kayan abincin da ake shigowa da su daga waje zai rage farashin kayayyaki a Nijeriya – Shugaban Kwastam
Dakatar da biyan harajin kayan abincin da ake shigowa da su daga waje zai rage farashin kayayyaki a Nijeriya – Shugaban Kwastam
Shugaban hukumar hana fasa kwauri a Nijeriya Kwastam, Bashir Adeniyi, ya ce dakatar da haraji kan kayan abinci da magunguna da ake shigowa da su daga kasashen waje zai rage farashin kayan abinci.
Ya bayyana hakan ne a ranar Talata a yayin wani taron ganawa da shugabannin tsaro a Abuja kan matakan da gwamnatin tarayya ta dauka na rage farashin kayan abinci.
Yace an shirya zanga-zanga ne akan abubuwa da dama, daya daga cikinsu shine kawo karshen hauhawar farashin kayayyaki”,Mun gano cewa ana shigo da abinci mai tarin yawa da ake amfani da shi a Najeriya. Don haka daya daga cikin abubuwan da shugaban kasa ya yi na rage tasirin farashin shigo da kaya shi ne dakatar da harajin kwastam da haraji kan kayan abinci da ake shigowa da su na wani lokaci.
“Mun yi imanin cewa idan aka aiwatar da hakan, zai taimaka wajen rage farashin kayayyakin abinci a kasuwanni.



