DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Sunday, April 12, 2026
Home Blog Page 408

Sojoji sun karbe mulki a kasar Bangladesh

Shekaru 15 da Fira-ministar Bangladesh ta kwashe taba mulkin kasar ya zo karshe a Litinin din nan, bayan da zanga-zangar da ke gudana a kasar ta ki ci, ta ki cinyewa.
Sheikh Hasina dai ta tsere ta bar kasar, yayin da sojoji suka bayyana karbe ikon tafiyar da kasar.
Sojojin karkashin jagorancin babban hafsan soji na kasar Waker-Uz-Zaman, sun ce za su kafa gwamnatin rikon kwarya.
Tun a farkon watan Juli dai aka fara zanga-zangar kin jinin gwamnatin Bangladesh da ta yi sanadiyyar mutuwar mutune kusan 100 a ranar Lahadi.
Fira-minista Hasina mai shekaru 76 dai ta fice daga kasar ne a jirgi mai saukar ungulu bayan da masu zanga-zanga suka cika fadarta.

Tirela 20 ta shinkafar da gwamnatin tarayya ta ce ta ba jihohi, ba ta iso hannunmu ba – Gwamnan Gombe

Gwamnatin tarayya ta sa kafa ta shure abin da ta kira ikirarin da Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya ya yi, na cewa har yanzu jiharsa ba ta karbi tirela 20 ta tallafin shunkafar da gwamnatin tarayyar ta ce ta rarraba wa jihohi ba.

Ministan yada labarai Mohammed Idris a wata hira da BBC Hausa kamar yadda jaridar Premium Times ta rawaito, ya ce babu jihar da ba ta karbi nata kason ba, ya zuwa yanzu.
Ministan ya ce tun makonni biyu da suka gabata aka kammala rarraba wannan tallafin shinkafa ga jihohin. Inda ya kara da cewa kowane Gwamna a Nijeriya ya tabbatar da amsar wannan tallafi ban da Gwamnan na jihar Gombe.
A Talatar makon jiya, aka jiyo Gwamna Mohammed Inuwa Yahaya a lokacin da yake ganawa da kungiyoyin fararen hula a jihar na cewa har yanzu wannan sakon tallafin bai zo hannunsu ba daga gwamnatin tarayya.

An garzaya da wasu iyalai asibiti bayan sun sha wani kunu

Wasu bayanai da jaridar Daily Punch ta samo daga jihar Benue sun ce an garzaya da wasu iyalai asibiti bayan sun sha wani kunu a yankin Egba, cikin karamar hukumar Agatu ta jihar Benue.
Bayanan sun ce lamarin ya faru ne kan wata mata da ba ta da miji mai suna Amina da ‘ya’yanta da wani jikanta, jimilla dai su shida ne aka ce sun sha wannan kunu da ya yi sanadiyyar cikinsu ya baci har aka garzaya da su asibiti.
Wani dan unguwarsu Amina ya shaida cewa iyalan sun fara zazzaga amai a gida bayan da suka sha kunun, daga nan aka garzaya da su asibiti.
Dan unguwarsu Amina de n ya ce lokacin da aka garzaya da su asibiti ba su san inda kansu yake ba saboda tsananin ciwo.

Masu zanga-zanga zasu sauya akãla zuwa birnin taraiya Abuja daga ranar Litini

Da alama masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren Gwamnatin Tinubu basu gamsu da jawaban da yayi ga ‘yan ƙasa ba, a maimakon kawo karshen gangamin, yanzu haka shirin shiga Abuja masu zanga-zangar suke.

Rahotanni sun nuna cewa masu gangamin suna wallafawa a shafin nan mai taken #OccupyAbuja cewa zasu dunguma kuma zuwa birnin taraiyar ƙasar domin cigaba daga inda suka tsaya.

Sauran wallafe-wallafe da aka yi ta yi a shafin na twitter ciki har da na tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyar African Action Congress Omoyele Sowore da sauran su, na nuna alamun zanga zanga zata yi zafi a Abuja.

Wasu mabiya addinin Kirista sun gudanar ibadar Lahadi a filin zanga-zanga a jihar Plateau

Ɗaruruwan masu zanga-zanga mabiya addinin kirista da suka saba Ibadar Lahadi a Coci, a wannan karon sun gudanar da wadannan addu’o’in nasu a matattarar zanga-zanga da ake a jihar Plateau.

Wannan ibada ta nuna hadin kai a fili, saboda a lokacin da suke wannan ibada mabiya addinin Musulunci ne ke kewaye da su suna basu kariya.

Ɗaya daga cikin limaman Cocin dake jagorantar majami’ar El-Buba Outreach Ministries da ke Jos, Pastor Isa El-Buba ya jaddada bukatar gwamnatin Najeriya ta kawo ƙarshen yunwa da rashin tsaro da suka addabi ‘yan ƙasar.

A ranar Juma’a ma anga yadda mabiya addinin kiristan suka bada tsaro ga Musulumai da ke Sallar Juma’a a lokacin zanga-zanga, wacce aka fara ta ranar Alhamis ɗaya ga watan Agustan nan da muke ciki

Amnesty International ta bukaci gwamnan Kano ya kafa kwamitin gano yadda zanga-zanga ta kazance a jihar

Ƙungiyar kare hakkin bil’Adama ta Amnesty International ta bukaci gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya gaggauta samar da kwamitin bincike da zai binciko dalilin da ya sa jami’an tsaro suka yi ajalin masu zanga-zanga mutum 10 a unguwar Kurna da Ƙofar Nassarawa
A wata sanarwa da Babban Daraktan Ƙungiyar a Najeriya Isa Sunusi ya tura wa DCL Hausa, Amnesty ta ce dole ne kuma kwamitin da gwamna Abba zai nada ya binciki irin yadda mu’amalar jami’an tsaro a Kanon ta kasance da masu zanga-zanga da kuma irin hatsaniya da kungiyar ke zargin wasu da aka dauki nauyinsu ne suka haifar, sa’annan ƙungiyar tana buƙatar a samu kwararru da za su yi aikin kuma a yi a bainar jama’a.
Amnesty ta jaddada cewa idan gwamnatin Kano ba ta yi wannan bincike ba, abin zai zamo ƙalubale babba ga tsarin doka, kuma babu abin da zai ƙãra haifar wa illa ƙarin aikata laifuka cikin ganganci wanda dama ke faruwa a Najeriya.

Mun sayo kayayyakin noma na zamani, don kawo ƙarshen yunwa a Nijeriya – Shugaba Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu ya sanar cewa gwamnati ta sayo kayan noma na biliyoyin Naira dan kawo ƙarshen yunwa a ƙasar.

Tinubu a jawabin da yayi ga ‘yan Najeriya Lahadinnan ya ce wannan mataki zai taimaka gãya wurin samar da wadataccen abinci mai rahusa a ƙasar.

Ya kuma ce yana ganawa da gwamnoni da wasu ministoci dan ganin an cimma hakan, sa’annan gwamnati ta raba taki ga manoma inji shugaba Tinubu dan cika wannan buri na gwamnati.

Tinubu ya ce ya fahimci tsanani da ya ingiza jama’a yin zanga-zanga amma duk da haka bai kamata a bari tashin hankali ya daidaita ƙasar ba.

Bama cikin wadanda suka yi ƙone ƙone a zanga-zangar Kano-Ƙungiyar Kano Peace Ambassadors

Ƙungiyarnan ta Kano state Peace Ambassadors mai fafutukar tabbatar da zaman lafiya ta nisanta kanta daga ƙone-ƙone da aka yi lokacin zanga-zanga da aka yi ranar Alhamis a Kanon.

Shugaban ƙungiyar Nasiru Usman Na’ibawa ya ce sun gudanar da zanga-zanga mai tsafta daga ofishin su da ke titin Aufu Baƙo zuwa fadar Sarki Sunusi, suka miƙa masa takardar koken jama’a.

Ya baiyana cewa sun so su mika wata wasikar kuma ga gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf amma shawarar da jami’an tsaro suka basu ya sa suka fasa.

Ya ce shugaba Tinubu yana bukatar ƙarin lokaci dan magance matsalolin ƙasar, yana kuma shawartar ‘yan Najeriya suka tsãme kansu daga zanga zangar da ake domin ta fara haifar da ɗa mara ido.

Shugaba Tinubu zai yi wa kasa jawabi a ranar Lahadi

Shugaban Najeriya Bola Ahmad Tinubu zai yi jawabi ga ‘yan Najeriya ranar Lahadi 4 ga watan Agustan nan da muke ciki.

A sanarwa da kakakin shugaban kasa Chief Njuri Ngelale ya fitar ta baiyana cewa ana bukatar kafafen yada labarai su jona daga tashar talbijin ta taraiya NTA da gidan radiyon taraiya FRCN domin watsa wannan jawabi na shugaban ƙasa ga ‘yan Najeriya.

Sanarwar ta ce shugaba Tinubu zai fara jawabin ga ‘yan ƙasa da misalin karfe 7:00 na safiyar ranar ta Lahadi sannan za’a maimaita jawabin nasa da misalin ƙarfe 3:00 na yamma da kuma ƙarge bakwai.

Wannan jawabi na shugaban ƙasa dai zai zo ne kwana ɗaya bayan da babbar jam’iyar adawa PDP ta caccaki shugaba Tinubun kan shuru da ya yi, a yayin da aka shiga rana ta uku ana yi wa gwamnatin sa zanga-zangar adawa da tsare-tsaren ta.

Shugaba Tinubu na bibiyar abubuwan da ke wakana game da zanga-zanga a Nijeriya – Bagudu

Ministan Kasafi da kula da lamurran tattalin arzikin Najeriya Atiku Bagudu ya ce shugaba Tinubu na nan yana bibiya tare da nazarin abubuwa da ke faruwa a zanga-zangar da ake yi wa gwamnatin sa.

An samu ƙiraye-kiraye kan shugaba Tinubu ya ce wani game da wannan zanga-zanga a yayin da ta shiga rana ta uku, abinda Bagudu ke cewa ai yana sane sarai da abubuwan da ke wakana.

Ministan ya amince cewa ‘yan Najeriya suka cikin mayuyacin hali, amma yana bada tabbacen shugaba Tinubu yana aiki tukuru da zummar ganin an sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya.