Gudun bara ko afka wa assha ya sa nake sayar da ruwa a ‘kura’ – Macen da ke tura kurar-ruwa a Kano
Malama Gambo Haruna, mace ce mai matsakaitan shekaru a birnin Kano da ta shafe shekaru sama da biyu tana tura kurar-ruwa domin sayar da ruwa ta samu abin da za ta ciyar da ‘ya’yanta 6.
Mijin Gambo dai, ya rasu ne shekaru kusan 6 da suka gabata.
Matar na zaune ne a wani gidan da ta kama hayar daki daya, inda take biyan kudi Naira 12,000 duk shekara a Gadar Katako Rimin Kebe cikin karamar hukumar Ungoggo jihar Kano.
Binciken Daily Trust ya gano cewa matar na cikin matsanancin halin rayuwa, ganin yadda a shekarunta bai kamata ta yi wannan tsufan ba.
Malama Gambo ta ce tana yin dukkanin mai yiwuwa don ganin ta samu abin da za ta ciyar da ‘ya’yanta don tana gudun ta yi bara ko shiga wata harkar da bata dace ba.
Ta yi imanin cewa duk halin da take ciki, Allah Ya sani, kuma zai fitar da ita.
Sai dai duk da wannan hali da Malam Gambo take ciki, bai hana ‘ya’yanta zuwa makaranta ba.
Shugaba Tinubu na cikin jerin musulman duniya 500 da ke da karfin fada a ji
Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu na daga cikin jerin sunayen mutane 500 musulmai da ke da karfin fada a ji a duniya.
Kazalika, akwai mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar da mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da karin wadansu ‘yan Nijeriya 12 da ke cikin jerin sunayen mutanen.
Wannan ne karon farko da aka ambato sunan shugaba Tinubu a jerin sunayen musulmai masu karfin fada a ji a duniya da cibiyar kula da harkokin addini ta kasar Jordan ke fitarwa duk shekara.
Sai dai, a wannan sabon bugun, an cire sunan tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari da ya ke yawan fitowa a duk lokacin da aka fitar da sunayen.
Shekh Habib Umar Bn Muhammad Bn Salim Bn Hafiz ne Musulmin da ya fi kowa karfin fada a ji a duniya.
Farkon Kannywood, karuwai ma kyamarta suke yi – Kamaye
Sanannen marubucin nan, mai shirya fim tare da ba da umurni, Dan Azumi Baba da aka fi sani da Kamaye ya ce lokacin da aka bude masana’antar shirya fim ta Kannywood karuwai ma kyamarta suke yi.
Kamaye da aka zanta da shi a shirin Gabon Talk Show ya ce a zamanin babu macen da ke son a ga fuskarta a fim, saboda ana zaton harkar shashanci ce kawai a ciki.
Dan Azumi Baba ya ce “an yi lokacin da idan muka je gidan karuwai neman wadda za mu saka a fim, sai karuwa ‘yar’uwarta ta hana, ta ce za ki shiga fim kamar dai ‘yar iska”.
Ya ce a zamanin, Hindatu Bashir wata tsohuwar jaruma a masana’antar ce kadai ke aminta ta fito a fim.
Atiku ya rubuta wa Hedikwatar BBC korafi bisa zargin bayar da labarin son zuciya kan ingancin takardun Tinubu
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya rubuta wa Hedikwatar BBC takardar korafi bisa zargin wuce gona da iri kan ingancin takardun Shugaba Tinubu.
A cikin wani kundi, BBC ta yi bayani dalla-dalla kan ingancin karatun boko na Bola Ahmad Tinubu. Binciken BBC dai ya sanar cewa babu inda shugaba Tinubu ya yi karya a takardunsa.
Sai dai mai magana da yawun Atiku Abubakar, Phrank Shaaibu a hira da ya yi da gidan talabijin na Channels, ya ce binciken BBC cike yake da son zuciya.
An rufe kasuwar Mile 12 International Market Lagos
Gwamnatin jihar Lagos ta umurci da a gaggauta rufe kasuwannin Mile 12 International Market, da Owode Onirin.
A cikin wata sanarwa daga daraktan hulda da jama’a na ma’aikatar muhalli ta jihar Kunle Adesina ta ce an rufe wadannan kasuwanni ne biyo bayan rashin tsafta da sauran karya dokokin da suka shafi muhalli.
Ya ce an rufe wadannan kasuwanni ne biyo bayan wani aikin hadin guiwa da jami’an LAWMA da na KAI suka gudanar biyo bayan umurnin da suka samu daga kwamishinan ruwa da tsaftar muhalli na jihar Tokumbo Wahab.
Sanarwar ta ce gwamnatin jihar Lagos ba za ta sassauta kan duk wani nau’in tara kazanta ba a ko’ina.
Ban tarar da ko sisi a lalitar Sokoto ba – Gwamna Ahmad
Gwamna Ahmad Aliyu na jihar Sokoto ya ce babu ko sisin-kwabo a lokacin da ya karbi ragamar tafiyar da jihar a matsayin Gwamna daga hannun Aminu Waziri Tambuwal.
Kazalika, Gwamnan ya ce babu wata takardar hannanta mulki da tsohuwar gwamnati ta bashi a lokacin da aka rantsar da shi.
Gwamna Ahmad na ba da amsa ne ga mataimakin shugaban majalisar wakilai Benjamin Kanu da ya tambaye shi yadda aka yi ya iya gabatar da ayyuka kusan 100 a cikin kwanakinsa 100 da rike ragamar tafiyar da jihar Sokoto.
Benjamin Kanu dai ya ziyarci Sokoto ne a ranar Alhamis a lokacin da ya je ziyarar ta’aziyya.
Gwamnan da ya yi magana ta hannun mataimakinsa Engr Idris Gobir ya ce kawai suna sadaukar da rayuwarsu ne don al’ummar jihar Sokoto su samu saukin rayuwa, amma dai ba su tarar da sisin-kwabo a cikin lalitar gwamnatin jihar kusan watanni biyar kenan.

