Monday, April 6, 2026
Home Blog Page 490

Maulud: Gwamnan Katsina Dikko na son mutane su yi koyi da kyawawan halayen fiyayyen halitta SAW

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya bukaci ‘yan Nijeriya daga kowane addini da su kaunaci juna a harkokinsu na yau da kullum.
A cikin wata sanarwa daga mai magana da yawun Gwamna, Ibrahim Kaula Mohammed da ya aike wa DCL Hausa ta ce yin hakan, zai sa a samu zaman lafiya hadin kai da kaunar juna a tsakanin ‘yan Nijeriya don samun al’umma daya mai neman makoma daya.
Malam Dikko Umaru Radda a sakon da ya aike da shi don bikin zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta manzon tsira sallallahu ta’ala alaihi wa sallim, na bana, ya bukaci mutane da su rubanya kwazonsu wajen aikata daidai da koyi da halaye na gari na fiyayyen halitta “SAW”.
“Manzonmu, manzon tsira sallallahu ta’ala alaihi wa sallim ya yi daban da sauran manzanni, wanda ya gudanar da rayuwarsa cikin kana’a da tausayin al’ummar duniya da tsantsar gaskiya da rikon amana da sauran halayen na ƙwarai”. Inji Dikko.

Mahaifiya ta kai danta kotu don yana barazanar kashe ta a Kano

Wata kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu jihar Kano ta tsare wani mutum da aka sakaya sunansa bisa zargin barazanar kisan mahaifiyarsa.
Mahaifiyar yaron dai ce ta maka dan nata kotu bayan da wata zazzafar muhawara ta barke a tsakaninsu.
Mahaifiyar dai ta roki kotu da ta umurci dan nata da ya tashi ya bar mata gida don tsaron rayuwarta.
Sai dai bayan da alkali ya karanta masa laifukan da ake tuhumarsa, dan matar duk ya musanta su.
Ya shaida wa kotu cewa, kawai dai saboda ya rabu da matarsa, kuma yanzu baya da kudi ne ya sa mahaifiyarsa take masa wannan zillar.
Alkalin kotun Khadi Isah Rabi’u Gademi Gaya ya umurci da a ci gaba da tsare yaron har sai ranar 25 ga watan Oktoba inda za a ci gaba da sauraren karar.

Gwamnatin Tinubu ta fusata kan kalaman Gwamnan Zamfara na cewa tana sulhu da yan bindiga a sirrance

0
Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya caccaki gwamnan jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, kan ikirarinsa na cewa gwamnatin tarayya na yin ganawar sirri tsakaninta da ‘yan bindiga a jihar.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Suleiman Haruna, ya fitar a Litinin din nan.
Sanarwar ta ce gwamnatin Nijeriya ta nuna rashin jin dadinta kan yadda gwamnan ya yi kalaman sakamakon cewa ya fito daga jam’iyyar adawa ta PDP.

Farashin buhun siminti zai iya kaiwa N9,000 a Nijeriya

Kungiyar masu harhada siminti ta Nijeriya ta ja kunnen cewa muddin gwamnatin tarayya ba ta tsahirta shirinta na amfani da tsarin zuba kankare a kan titunan da ake ginawa ba, to farashin siminti zai iya kai wa Naira 9,000 a kasar.
A halin da ake ciki dai, ana sayar da jikkar simintin mai nauyin kilogram 59 kan kudi N5,000 ko fiye a wasu wuraren.
Kazalika, kungiyar ta ja hankalin cewa akwai bukatar gwamnati ta sa baki wajen yawan tashin farashin da simintin ke yi a ‘yan kwanakin nan ta hanyar kai dauki a masana’antar sarrafa simintin.
Kungiyar a cikin wata sanarwa daga Shugabanta Prince David Iweta da Sakatare Reagan Ifomba, ta yaba wa ma’aikatar aikace-aikace ta tarayya da take kokarin yin amfani da simintin a wajen gine-ginen hanyoyi, sai dai ta ja kunnen cewa yawan amfani da simintin zai sa a rika nemansa a kai a kai da kuma hakan zai sa ya yi tsada a kasuwa.

Burin Dikko Radda shi ne kowa ya tsaya da kafafunsa – Abdullahi Garba Faskari

Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Barr Abdullahi Garba Faskari ya ce burin Gwamnan jihar Malam Dikko Umaru Radda shi ne kowa ya dogara da kansa.
Ya ce yin hakan zai taimaka mutane su samu ingantattar rayuwar da ta dace.
Barr Abdullahi Garba Faskari na magana ne a Funtua a wajen kaddamar da shirin wayar da kan al’umma game da alfanun da ke tattare da tashar kula da shige da ficen kaya ta kan tudu wato Funtua Inland Dry Port a garin Funtua jihar Katsina.
Sakataren Gwamnatin jihar ya ce gwamnatin jihar ta samar da fili murabba’in kadada 77 domin gina wannan tasha a matsuguni na dindindin domin samun ingancin shige da ficen kaya yadda ya kamata.
Ya misalta cewa fadin fili murabba’in kadada 77, shi ne kwatankwacin filin kwallo 77 ta yadda wurin zai wadatar da duk abin aka shigo ko za a fita da shi daga Nijeriya.
Barr Abdullahi Faskari ya ce hakan zai samar wa da dumbin mutane ayyukan yi da hakan zai sa tattalin arzikin jihar Katsina da na Arewa da ma na Nijeriya bakidaya ya bunkasa.
Ya ce dama tuni burin Malam Dikko Umaru Radda shi ne ya ga mutane sun samu hanyoyin da za su dogara da kansu ta yadda gwamnati za ta yi duk abin da ya kamata domin ta tallafa musu.

Kotu ta kwace kujerun ‘yan majalisa uku na PDP a jihar Filato

0

‘Yan majalisar dokokin da kotun sauraran kararrakin zaben ta rusa zabensu tare da mika nasara ga APC da LP sune Remvyat Nanbol da Agbalak Adukuchill da kuma Happiness Akawu da ke wakiltar Langtang central da Rukuba/Iregwe da kuma Pengana.
Jaridar Daily Trust ta ce wannan na zuwa ne kwana guda kafin kotun ta yanke hukunci tsakanin APC da PDP a zaben gwamnan na jihar ta Filato.

Fallen atamfa ya yi sanadiyyar rasuwar wani mutum a Kano

Wani mutum mai shekaru 37 mai suna Usman Ayuba ya riga mu gidan gaskiya a lokacin da ya shiga wata rijiya don dauko atamfar wata mata da ta fada a ciki.
Lamarin ya faru ne a yankin Kawon Maigari na karamar hukumar Nassarawa a jihar Kano.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Saminu Abdullahi ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN, inda ya ce lamarin ya faru ne da yammacin Talata.
Jami’in ya ce sun samu labarin cewa wata mata ce ta bukaci Usman da ya shiga rijiyar domin dauko mata fallen atamfarta da ya fada a ciki.
Bayanai sun ce mutin ya rasu ne ta dalilin karancin iskar shaka a cikin rijiyar.

Ranar sanin makoma a Kano

0

Ranar Sanin Makoma! Ita ce kalmar da ta kusan yin dai-dai da zama taken wannan rana a wajen mutanen jihar Kano.

Kowanne lokaci daga yanzu, kotun dake sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Kano za ta yanke hukuncin da zai tabbatar da mafarkin ‘yan “Gawuna is Coming ko kuma Kwankwasiyya zama daram.

Jihar Kano na cikin jihohin da jam’iyyun adawa suka maka jam’iyya mai ci a gaban kotu inda suke nuna shakku game da cin zaben, duk da dai bangaren jam’iyyar NNPP da ta lashe zabe na ganin zaben nasu halastacce ne.

Shin wai mene ne dalilin da ya sa jam’iyyun biyu ke nuna wa juna yatsa a game da sahihancin zaben?

Da farko jam’iyyar APC mai adawa na bukatar kotu ta rushe zaben bisa wasu dalilai da suka hadar da aringizon kuri’a, da kuma rashin chanchantar dan takara Abba Kabir Yusuf da kuma rashin kasancewarsa cikin jerin mutanen da ke neman takarar gwamnan jihar Kano a lokacin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bukaci a mika.

A yayin zaman sauraren shari’ar, lauyan jam’iyyar APC Abdul Fagge ya gabatar da shaidu guda 32 da suka hadar da matsalolin da aka rika samu a gurin tantance masu kuri’a da ma yadda aka daina amfani da nau’urar a wasu gurare a lokacin zaben.

Haka kuma ya gabatar da takardun sakamakon zabe a matakin mazaba da kananan hukumomi, wadanda alkalumansu, suka sha bambam da wadanda hukumar zabe ta jihar Kano ta sanar.

Baya ga kalubalantar sakamakon zabe da aikata ba dai-dai ba, lauyan jam’iyyar ta APC ya kuma kalubalanci ingancin takardun Kammala karatu na gwamna Abba Kabir Yusuf.

Yayin da ya ke mika wa kotu shaidunsa na karshe, Lauya Fagge, ya zargi jamiyyar NNPP da yi wa dokar zabe ta 2022 karan tsaye, kasancewar sam Abba ba ya cikin ‘yan takara, katsam kawai aka gan shi daga sama, ma’ana dai har lokacin da hukumar INEC ta kammala karbar sunayen ‘yan takara jam’iyyar NNPP ba ta aike da sunan Abba a matsayin dan takararta ba.

A binciken da DCL Hausa ta gudanar cikin kundin dokokin zabe ta gano cewa sashe na 72 ya fayyace cewa dole ne jam’iyya ta aike wa INEC rajista da kuma sunan dan takararta kwanaki 30 kafin gudanar da zaben cikin gida.

A cikin bayanin da Lauya Abba ya yi, ya  gano cewa akwai takardun kada kuri’a guda dubu 270 da aka samu sun lalace, kuma babu tambarin hukumar INEC a jikinsu amma duk da haka aka kirga su a matsayin cewa Abba aka zaba, sannan ya ci gaba da cewa hukumar INEC ta ayyana zaben ‘yan majalisar jiha guda 15 a matsayin wadanda ba su kammala ba, kuma an yi su ne lokaci guda da na gwamna, don haka matukar an samu matsala a na dan majalisa ya zama wajibi a samu a na gwamna.

A karshe dai lauya Abdul Fagge na bukatar kotu ta ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, wato dai kalmar  “INCONCLUSIVE”  da wasu ke ganin kan razana magoya bayan Kwankwasiyya ta tabbata.

                                     Matsayar NNPP

To amma duk wannan dogon turanci da lauyan APC ke yi tamkar dai waka ce a kunnuwan lauyan jam’iyyar NNPP Bashir Tudunwuzurci, wanda ke bukatar kai tsaye kotu ta yi watsi da wadannan hujjoji da ya ayyana a matsayin ba ta lokaci.

A cewarsa, idan aka yi la’akari da irin ratar da jam’iyyar NNPP ta bai wa APC  yawan kuri’un da aka  kada  tabbas cin zarafi ne ma APC din ta shigar da kara.

Lauya Tudun wuzurci ya dage kan cewa sunan Abba na  nan cikin takardar da aka mika wa hukumar INEC kuma an mika ta a kan lokaci kamar yadda doka ta tanada, yana mai cewa tuni kotun koli da ke saurarar kararrakin kafin zabe ta yi watsi da wannan kara ta rashin sunan Abba cikin jerin ‘yan takara.

Kan batun kuri’u fiye da 270 da ba su da tambarin hukumar INEC da APC ke ikirarin an zabi Abba da su, Lauyan ya ce jam’iyyar APC ta gaza gabatar da samfurin takardun a gaban  kotu, kuma babu wata mazaba a fadin jihar Kano da aka sami wannan korafi sai a yanzu ake jin labari.

Sai dai binciken da DCL Hausa ta sake yi kan wannan batu a cikin kundin dokar zabe ta 2022, ta ce ko da babu tambarin hukumar INEC a jikin takardar zabe, matukar kwamishinan zabe ya kirga ta, to tabbas za a dauke ta a matsayin mai inganci.

Lauyan jam’iyyar NNPP ya roki kotun da ta yi watsi da bukatar APC na ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, a cewarsa, idan aka yi la’akari da yawan mutanen da suka fita zaben, babu makawa za a gane ingancin yawan kuri’un da Abba ya samu.

Hukumar dai ta sanar da Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP  a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’a 1,019,602, abin da ke nufin ya samu nasara kan babban abokin takararsa na jam’iyyar APC Dr Nasir Yusuf Gawuna wanda ya sami kuri’a 890,705. 

Yanzu mutane a cikin da wajen jihar Kano sun zura ido su ga irin hukuncin da kotun sauraran zaben ta yanke. Amma masu sharhi na cewa maganar zargin magudi ba za ta mutu a nan ba, domin babu alamun duk bangaren da hukuncin bai yi wa dadi ba, zai rungumi kaddara ya tari gaba, inda tuni wasu ke cewa komi wuya ko rintsi, da alama kotun koli za ta iya tabbatar da “Gawuna is Coming” ko kuma “Kwankwasiyya Daram”

Jigon APC ya lakada wa kwamishina dukan tsiya

Shugaban jam’iyyar APC na wata mazaba a jihar Ondo Mr Olumide Awolumate ya yi bayani tiryan-tiryan dalilin da ya sa ya lakada wa kwamishinar mata da walwalar jama’a ta jihar dukan tsiya.
Ya ce sa’in-sa ce ta kaure tsakaninsu, da ta kai su ga dambacewa da Mrs Juliana Osadahun.
Bayanan da jaridar Punch ta tattara sun ce cacar bakin da ta kai ga kai dukan ta faru ne a wajen rabon kayan tallafin rage radadin tsadar rayuwa a karamar hukumar Arigidi Akoko ta jihar ta Ondo.
Bayanai sun ce jigon na APC Awolumate har ya raunata kwamishina Osadahun a kai. Sai dai rahotanni sun ce tuni uwar jam’iyya ta jiha ta dakatar da wannan shugaban jam’iyya na mazaba.

Nijeriya na bukatar karin azuzuwa 907,769 a makarantun bokon kasar – UBEC

Shugaban hukumar kula da ilmin firamare ta Nijeriya UBEC Dr Bobboyi Oyeyemi ya ce kasar na bukatar karin makarantun boko 20,000 da azuzuwa 907,769. 
Dr Bobboyi ya ce sai an yi hakan sannan a yi nasarar magance matsalar yaran da ba su zuwa makarantun boko.
Shugaban hukumar na magana ne a lokacin da hukumomin da ke karkashin ma’aikatar ilmi ta kasa suke ganawa da ministan ilmi Prof Tahir Mamman a Abuja.
Dr Bobboyi ya sanar da ministan cewa akwai karancin gine-gine da ma’aikata da ake bukatar a cike gibin muddin ana so a yi nasarar samar da ilmi mai inganci ga yara.