Monday, April 6, 2026
Home Blog Page 499

Gini mai bene hawa 2 ya rufta kan mutane a Abuja

0

Yanzu haka wasu mutane a Abuja na karkashin baraguzan wani gini da ya ruguje a Abuja. Jaridar Daily Trust wacce ta ruwaito wannan labarin ta ce bene ne mai hawa biyu da ke layin Lagos Street a Unguwar Garki. Kawo yanzu babu wani karin haske a kan aikin ceto rayukan mutanen a wannan al’amari da ya faru a safiyar Alhamis.

Sojojin mulkin Nijar sun sauke shugabannin jami’o’in Agadez da Zinder

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun cire shuwagabannin jami’o’i biyu daga mukamin su
A cikin wata sanarwa ce da suka fitar hukumomin mulkin sojan Nijar suka bayyana cire wasu malaman jami’a daga mukamman da suke rike da su a cikin jami’o’in daban daban ciki kuwa har da shuwagabannin jami’o’in Agadez da Zinder 
Wannan na zuwa ne kwanaki biyu bayan da wani gungunsu na malaman jami’ar da ya kunshi malaman 37 ya fitar da wata sanarwa wacce a ciki suka nisanta kansu da wata sanarwar ta daban da kungiyar ta SNECS ta fitar wacce a ciki ta kawo goyan bayan ta da sunan dukkan malaman ga sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar
Shi dai wannan gungu na malaman jami’ar ya ce ko alama ba ya goyan bayan wannan juyin mulki
Kazalika wata sanarwar ta daban da kakakin gwamnatin rikon kwaryar ta Nijar ya karanta na cewa an kawo karshen aikin sakataren ma’aikatar ilimi mai zurfi tare da shugaban hukumar da ke kula da jarabawar Baccalauréat da ake kira da OBEECS
Wasu rahotannin kuma na cewa tuna aka kira daya daga cikin malaman Pr Malaman Issa an kiraye shi ofishin jami’an tsaron na Gendarmerie

Ministocin Tinubu za su lakume Naira bilyan 8.6 matsayin albashi

Gwamnatin Shugaba Tinubu za ta kashe kudi Naira bilyan 8.6 wajen biyan albashi da alawus-alawus cikin shekaru 4 na ministoci 48 da aka nada.
Daily Trust ta rawaito cewa jimillar kudin ta kai haka ne bayan da hukumar tattarawa da rarraba kudaden shiga ta kammala bitar albashi da alawus-alawus na manyan ma’aikatan gwamnati.
Sai dai wani kwararru a bangaren tattalin arziki ya sanar da manema labarai cewa yawan kudin ya ci karo da kudiri ko jawabin Shugaba Tinubu na farko, da ke cewa zai rage yawan kudaden da ake kashewa jami’an gwamnati.
Kwararrun suka ce nada wadannan ministocin da yawa, shi zai sa su ma su nada masu taimaka musu na musamman da hakan zai kara nauyi ta gwamnati.
Lokacin farko dai kenan da aka samu yawan ministoci a Nijeriya sun kai 48 tun 1999 da aka dawo dimokradiyya. Zamanin tsohon shugaban kasa Buhari na da ministoci 42.
Tsohon shugaban kasa Good luck Jonathan na da ministoci 33 sai Marigayi Umaru Musa Yar’adua ya yi ministoci 39. Shi kuwa tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya yi ministoci 42.

Ba zan iya sayar da “manpower” ko kayan mata a Saudiyya ba – Sadiyya Haruna

Sadiyya Haruna ta ce ba za ta iya sayar da kayan da take sayarwa a Nijeriya a kasar Saudiyya ba. 
A cikin gajeran bidiyo da ta wallafa, ta ce, ta gode da arzikin da Allah ya yi mata a Nijeriya; ba ta bukatar daukar maganin maza da kayan mata zuwa kasa mai tsarki. 
Fitacciya a shafukan sada zumunta da aka jima ana zargin ta da batsa ta hanyar sayar da wadannan kayayyaki na shan cece-kuce a baya-bayan nan a kan tangardar da aurenta da mawaki G-Fresh ke fuskanta.
A wata hira da Sadiyya Haruna ta yi da DCL Hausa a 2021, ta ce, ba ta jin kunyar wadannan kayayyaki da take sayarwa.

Tsageranci ne a sake gurfanar da ni a gaban kotu-Hudu Ari

0

Dakataccen
kwamishinan zaben jihar Adamawa Barista Hudu Ari ya maka kungiyar lauyoyi ta kasar
a gaban kotu bayan kishin-kishin din da suke yi na  sake gurfanar da shi a gaban kotu.

 

Ari
na wannan barazana ne, bayan da kungiyar ta NBA ta fara
 yunkurin sake gurfanar da shi a gaban kotu kan
zargin yunkurin karkatar da sakamakon zabe, bayan karbar na goro.

A cewar
Ari babu wata hujja da kungiyar ta ke da ita na sake gurfanar da shi a gaban
kotu, kasancewar waccan kotun da aka kai shi ta bada umarnin a tsaya a inda ake
har sai ta kammala binciken da ta ke yi.

Ari ya ci gaba da cewa tsageranci ne ga
kotu idan suka sake gurfanar da shi kan laifi guda, don haka ya bukace su da
kada su kuskura su fara, matukar ba haka ba kuma ta tabbata suma basa mutunta
aiki su.

Tun farko dai ana zargin
Yunusa Ari da ayyana Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar
Adamawa alhali ba’a ma kammala girka sakamakon zabe ba, dalilin da ya sa aka
rika yada jita-jitar cewa ya karbi cin hancin kudade har naira biliyan guda.

Wannan dalili ne ya
sa hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya ta sanar da dakatar da shi daga
aikin sa sannan kuma aka gurfanar da shi a gaban kotu, sai dai kuma fara shari’ar
ke da wuya kotu ta bukaci a dakata har sai an kammala bincike.

 

Abinda na gaya wa Shugaba Tinubu kan ziyarata a Nijar – Abdulsalami Abubakar

0

Tsohon shugaban
Najeriya Abdulsalam Abubakar ya sanar da mikawa shugaban kasar Bola Ahmad
Tinubu rahoto kan batutuwan da suka tattauna yayin ziyarar tawagar da ya
jagoranta zuwa jamhuriyar Nijar.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan
kammala ganawar sa da shugaban kasa, Abdulsalam Abubakar ya ce dukkanin alamu
sun nuna cewa yaki ba zai shawo kan al’amarin ba, a maimakon haka kamata ya yi
a rungumi tattaunawar diplomasiyya.

Ganawar ta su ta sami halarcin shugaban majalisar
zartaswar kungiyar ECOWAS Dr Omar Touray da kuma babban mai baiwa shugaban
Najeriya shawara kan harkokin yada labarai Malam Nuhu Ribadu.

Bayan kammala ganawar ta su, shugaban Najeriya Tinubu
wanda kuma shine shugaban ECOWAS ya sha alwashin yiwa rahoton Nazari na tsanaki,
kafin daga bisani kuma a san matakin da za’a dauka.

Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ECOWAS ta
sanar da cewa ta gama duk wani shiri na fadawa Nijar da yaki.

 

Sojojin Najeriya sun ceto karin dalibar Chibok

0

Rundunar sojin Najeriya karkashin Operation Hadin kai sun sanar
da ceto karin dalibar Chibok guda daya.

 

Dalibar na cikin daliban Chibok 276 da ‘yan Boko Haram suka yi
garkuwa da su a ranar 14 ga watan Afrilun 2014 a cikin makarantar su da ke
kauyen Chibok na jihar Borno.

 

Da
yake Karin haske kwamandan rundunar Manjo Janar Gold Chibuisi ya ce bayan likitoci
sun kammala gwaje-gwaje akan dalibar mai suna Mary Nkeki, ya mikata ga hannun
kwamishinan harkokin mata ta jihar Borno Hajiya Zuwaira Gambo. Dalibar mai shekaru
27 ta kubuta daga hannun Boko Haram din ne tare da mijinta wanda shi dan Boko
Haram ne amma ya mika kai ga rundunar sojin mai suna Adamu. 
Bayanai sun nuna cewa sojojin sun yi nasarar gano Mary da
mijinta ne akan iyakar Najeriya da Kamaru a kokarin da suke yi na guduwa daga
sansanin ‚yan Boko Haram din, bayan da mijinta ya kuduri aniyar ajiye makamin
sa. 
Kafofin yada labaran Najeriya sun ruwaito cewa
Mary ta haifi yara guda biyu, sai dai sun mutu a sakamakon matsanaciyar cutar
yunwa da ta kama su lokacin da suke cikin dajin Gulumba dake karamar hukumar
Bama ta jihar Borno.

 

 

Burkina Faso ta taimakawa Nijar da motoci 300 na kayan abinci

0

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa manyan motocin
daukar kaya fiye da 300 daga Burkina Faso sun isa birnin Niamey a kokarin da kasar ke yi na ragewa yan Nijar radadin takunkuman da aka Sanya musu. 

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da kasashen Benin da
Najeriya manyan kasashen da ake shigar da abinci jamhuriyar Nijar suka rufe
iyakar su da kasar wadda ke karkashin juyin Mulki.

Tun bayan juyin mulkin na
Nijar ta ke samun goyon bayan gwamnatin kasashen Burkina Faso da Mali, abinda masana
ke ganin hakan yana da alaka da kasasancewar su sojoji.

Bayanai sun ce motocin makare
da kayan abincin sun sami rakiyar sojojin Burkina Faso, kafin daga bisani suka
mikasu hannun sojojin Nijar akan iyakar kasashen biyu.

Ko da yake jawabi daraktan
hukumar hana fasa kwauri ta jamhuriyar Nijar Kanal Adamou Zaraoumeye yace hukumar
sa ta karbi motoci guda 300 makare da kayan abinci da suka hadar da masara da
gishiri da sauran kayan masarufi.

A cewar sa nan ba da jimawa
ba za’a far araba ayan ga jama’ar kasar da nufin rage musu radadi.

 

 

An garzaya da kocin Man City Guardiola Asibiti

Mai horar da ‘yan wasan kungiyar Manchester City Pep Guardiola ba zai samu jagorancin kungiyar ba har na wasanni biyu da za ta buga nan gaba sakamakon wata tiyatar gaggawa da za a yi masa a gadon bayansa.
Guardiola wanda yanzu haka yana Barcelona inda aka yi masa tiyata yana kuma murmurewa ana sa ran ba zai jagoranci City ba a wasannin da za ta yi da Sheffield United a wannan Lahadi da Fulham a ranar 2 ga Satumba ba, inda mataimakinsa Juanma Lillo zai maye gurbinsa na wucin gadi.
City ta ce kocinta wanda ya jagoranci yan wasanta suka lashe kofina uku rigis a kakar da ta gabata na fama da “matsanancin ciwon baya na ” kuma tuni aka fita da shi zuwa birnin Barcelona don domin yi masa tiyata.

AU ta kori jamhuriyar Nijar daga cikin ta

0

Kungiyar tarayyar Africa ta sanar da korar
jamhuriyar Nijar daga cikin ta, abinda ke zama wani hukunci na baya-bayan nan
da aka yankewa Nijar bayan juyin Mulkin watan jiya.

Bayan taron kungiyar na yau Talata a
birnin Addis Ababa, kungiyar ta ce daukar wannan mataki ya zama wajibi la’akari
da yadda sojojin na Nijar suka ki bada hadin kan da ya dace a game da
tattaunawar Diplomasiyya.

Matakin na AU na zuwa ne bayan da tuni
ECOWAS da wasu kungiyoyin kasashen ketare suka sanar da kakabawa Nijar din
takunkumai, wadanda tuni suka fara tasiri a kanta.

Sai dai kuma masana na ganin
cire Nijar daga cikin AU ba zai yi mata wani tasiri ba, la’akari da yadda kungiyar
ke zama tamkar dai ‘yar amshin shatan kasashen yamma a wasu lokutan.

Bayan wannan
mataki, kungiyar ta AU ta kuma ce zata bibiyi irin matakan da kungiyar ECOWAS
ko CDEAO ta dauka kan jamhuriyar Nijar, don ganin ta inda ya kamata ta kara
shiga da nufin kara matsa lamba ga sojojin na Nijar.