Monday, April 6, 2026
Home Blog Page 9

Gwamnan Adamawa ya saka dokar takaita zirga zirga a karamar hukumar Lamurde

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya sake saka dokar hana fita ta awa 24 a karamar hukumar Lamurde, sakamakon sake barkewar hare-hare da tashin hankali ga wasu al’ummomin yankin.

Mai magana da yawun gwamnan, Humwashi Wonosikou, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin a birnin Yola.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnati ta dauki wannan mataki ne bayan sake samun rikice-rikice da suka haddasa asarar rayukan wasu mazauna yankin.

Majalisar dokokin jihar Rivers sun fara tantance sunaye sabbin kwamishinoni

‘Yan majalisar dokokin jihar Rivers sun fara tantance sunayen mutanen da gwamnan jihar Siminalayi Fubara ya gabatar domin nada su a matsayin kwamishinoni.

Rahotanni sun nuna cewa mutum tara ne aka raka zuwa majalisar da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin domin fara tantance su.

Mutanen da aka gabatar sun hada da Datonye Alasia, Tonye Bellgam, Temple Nwofor, Peters Nwagor, Charity Deemua, Tamuno Williams, Lekue Kenneth, Otonye TKD Amachree, da kuma Amairigha Hart.

A cikin wani bidiyo da tashar Arise TV ta watsa, an ga kowane daga cikin wadanda aka gabatar yana hawa mumbari yana gabatar da kansa tare da amsa tambayoyin ‘yan majalisar.

Joan Laporta ne ya hana Lionel Messi dawowa Barcelona don kauce wa rikicin shugabanci — Xavi Hernández

Tsohon kocin kungiyar Barcelona, Xavi Hernández, ya bayyana cewa shugaban kulob din a wancan lokaci, Joan Laporta, ne ya hana dawowar fitaccen dan wasa Lionel Messi kungiyar a shekarar 2023.

Xavi ya bayyana hakan ne a wata hira da jaridar La Vanguardia, inda ya ce bayan Messi ya lashe 2022 gasar kofin duniya, ya tuntube shi a watan Janairun 2023 kuma ya nuna sha’awar komawa Barcelona.

A cewarsa, kungiyar ta riga ta samu amincewar La Liga ta domin kammala cinikin dawowar Messi, amma daga baya shugaban kulob din ya dakatar da shirin.

Ya ce Laporta ya gaya mai kai tsaye cewa idan Messi ya dawo, zai iya haifar da rikicin iko a kulob din, kuma ba zai bari hakan ta faru ba.

Muna kira da a gaggauta tabbatar da dokar ta ɓaci kan tsaro a aikace – Sanata Ali Ndume

Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bukaci shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar da cewa dokar ta ɓaci da aka ayyana kan tsaro ta zama tana aiki a zahiri, ba magana kawai ba.

Ndume ya bayyana hakan ne bayan harin da ‘yan ta’adda suka kai garin Ngoshe, inda aka halaka mutane da dama tare da sace sama da mata da yara 100.

Sanatan ya bukaci gwamnatin tarayya ta kaddamar da hare-haren tsabtace yankuna da ake zargin ‘yan ta’adda na boyewa, musamman a dajin Sambisa da sauran dazukan da ke fama da matsalar tsaro.

Peter Obi ya soki shugabannin Nijeriya kan rashin mayar da hankali kan matsalar tsaro

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, ya soki shugabannin Nijeriya saboda, sun fi mayar da hankali kan zaɓen da ke tafe maimakon magance matsalar tsaro da ke ƙara tsananta a ƙasar.

A wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na sada zumunta, Obi ya ce ƙasar na cikin mawuyacin hali na tsaro, inda hare-haren ‘yan ta’adda da sace sacen mutane ke ƙaruwa a sassa daban-daban.

Ya kawo misali da hare-haren baya bayannan da aka kai jihar Borno da ya yi sanadiyyar mutane da dama tare da sace mata kusan 100.

Obi ya kuma nuna damuwa kan rahotannin matsalar tsaro a jihohin Nasarawa, Kogi da Benue inda mazauna yankuna ke cewa ‘yan ta’adda suna mamaye gonaki da dazuka, lamarin da ke tilasta wa mutane barin gidajensu.

Ana zargin tsohon ministan tsaro Badaru na shirin barin APC

Tsohon gwamnan Jigawa kuma tsohon ministan tsaro, Muhammed Badaru Abubakar, na fuskantar jita-jitar cewa zai iya barin jam’iyyar APC.

Hakan ya biyo bayan rashin ganinsa a taron jam’iyyar APC a jihar da kuma ganawarsa da wasu ‘yan adawa kamar Sule Lamido da Mustapha Lamido.

Kodayake jaridar Daily Trust ta ambato Badaru ya musanta shirin sauya jam’iyya, yana cewa ganawar da aka gani na iya kasancewa ne kawai a matsayin ziyara ko tuntuba.

Gwamnatin jihar karkashin ta bakin mai magana da yawun gwamna Umar Namadi, Hon. Hamisu Gumel ta ce ko da Badaru ya bar jam’iyyar, APC ba za ta rasa karfinta ba a jihar.

Najeriya na iya kara ganga 150,000 na mai a rana – NNPCL

Shugaban kamfanin mai na NNPCL, Bayo Ojulari, ya ce warware rikicin OPL 245 zai ba Najeriya damar kara ganga 150,000 na mai a rana.

Ya bayyana cewa hakan zai bai wa aikin Zabazaba–Etan deepwater project damar fara aiki.

Gwamnatin Nijeriya ta kulla yarjejeniya da Eni da kuma Nigerian Agip Exploration Limited domin kawo karshen rikicin mai na sama da shekaru 15.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ce warware matsalar na nuna wa masu zuba jari na duniya cewa Najeriya na shirye ta magance tsoffin matsaloli tare da bude damar sabbin kafofin zuba jari a bangaren makamashi.

Barayin daji sun yi sabuwar ta’asa a jihar Sokoto

Rundunar ‘yan sanda a jihar Sokoto ta tabbatar da cewa mutum daya ya rasa ransa yayin da mutane biyar suka shiga hannun ‘yan bindiga a kauyen Mallamawar Yari da ke karamar hukumar Rabah.

Mai magana da yawun rundunar, Ahmed Rufai, ya ce harin ya faru ne a daren Asabar, inda maharan suka kai farmaki garin.

Jaridar Punch ta ambato ya kuma musanta jita-jitar cewa maharan sun sanya hijabi domin boye kansu.

‘Yan sanda sun ce wadanda aka sace sun hada da mata uku da maza biyu, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da kokarin ceto su tare da kamo wadanda suka aikata laifin.

An warware rikicin rijiyar mai ta OPL 245 – Gwamnatin Nijeriya

Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, ya ce warware rikicin rijiyar mai ta OPL 245 zai taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Nijeriya da kuma karfafa kudaden shiga na gwamnati.

Ya bayyana hakan ne bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar da ta kawo karshen rikicin da ya shafe sama da shekaru 20, tsakanin gwamnatin tarayya da kamfanonin Eni da Nigerian Agip Exploration Limited a Abuja.

Fagbemi ya yabawa shugaba Bola Ahmed Tinubu kan jagoranci da ya nuna wajen bada umarnin a warware rikicin cikin lumana domin amfanin al’ummar Najeriya.

Paparoma Leo na XIV, ya yi addu’ar zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya

Paparoma Leo XIV ya yi addu’a a ranar Lahadi cewa ƙarar fashe-fashe da ake samu a Gabas ta Tsakiya za ta dakata, yayin da rikicin da ya biyo bayan hare-haren sama na Amurka da Isra’ila a Iran ke shiga rana ta tara.

Ya nuna damuwarsa kan yaduwar tashin hankali da tsoron cewa wasu ƙasashe, ciki har da Lebanon, na iya fada wa cikin rashin tsaro.

A baya ma, gidan talabijin na Channels ya ambato shugaban darikar Katolikan ta Duniya na kira ga shugabannin kasashen da abun ya shafa su daidaita tsakaninsu ta hanyar sulhu.