Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiRikicin PDP na ƙara zurfafa tsakanin bangaren Wike da Turaki

Rikicin PDP na ƙara zurfafa tsakanin bangaren Wike da Turaki

Tsagin PDP na Tanimu Turaki ya ɗaukaka ƙara kan rushe taron PDP na Ibadan na jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida Alhaji Tanimu Turaki.

Sun yaɗaukaka ƙarar ne kan hukuncin babbar kotun tarayya da ta soke taron jam’iyyar na ƙasa da aka gudanar a Jihar Oyo, a ranar 15 ga Nuwamba, 2025.

Da yake magana da ’yan jarida ranar Juma’a, Shugaban kwamitin gudanarwa na PDP Alhaji Tanimu Turaki ya ce duk da hukuncin kotu, jam’iyyar tana nan daram bisa doka, kuma ba ta girgiza ba, yayin da take jiran hukuncin kotun ɗaukaka Ƙara.

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Ibadan, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Uche Agomoh, ta yanke hukuncin soke taron ƙasa na PDP da aka yi a Ibadan, tare da umartar Turaki da sauran mambobin NWC da su daina bayyana kansu a matsayin shugabannin jam’iyyar na ƙasa.

Kotun ta kuma tabbatar da Kwamitin Rikon Ƙwarya ƙarƙashin jagorancin Mohammed Abdulrahman da Samuel Anyanwu a matsayin sahihin NWC har sai an gudanar da ingantaccen taron ƙasa.

Gwamnonin PDP sun mara wa taron Ibadan baya, inda aka zaɓi Turaki da sauran mambobin NWC na wa’adin shekaru huɗu. Sai dai Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, tare da Abdulrahman da Anyanwu, sun nace cewa su ne shugabannin rikon ƙwarya na jam’iyyar, inda suka kafa kwamitin mutum 13 a ranar 8 ga Disamba, 2025, da wa’adin kwanaki 60, duk da cewa an riga an tsara mika mulki daga tsohon shugaban PDP na ƙasa, Umar Damagum, kafin wa’adinsa ya ƙare a ranar 9 ga Disamba.

Sabani tsakanin ɓangarorin biyu ya kai ga ƙin amincewar Hukumar zaɓe mai zaman Kanta ta Ƙasa INEC da kowanne ɓangare, lamarin da ya haddasa shigar da ƙara da dama a kotu yayin da ake shirin tunkarar zaɓen 2027.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata